ASUU Ta Koka kan Rashin Cika Alkawari, Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki a Jami'o'i 11 a Najeriya

ASUU Ta Koka kan Rashin Cika Alkawari, Ta Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki a Jami'o'i 11 a Najeriya

  • Kungiyar ASUU ta soki gwamnatocin jihohi akalla bakwai kan rashin cika yarjejeniyar da aka cimmawa tsakaninta da gwamnatin tarayya a 2025
  • ASUU ta yi barazanar shiga yajin aiki a jami'o'i 11 da ke wadannan jihohi matukar aka gaza biyan haƙƙokin malamai daga nan zuwa karshen watan Yuli
  • Ta yi kira ga gwamnonin jihohin da abin ya shafa da su gaggauta aiwatar da yarjejeniyar tare da biyan dukkan basussukan da ake bin su

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Kungiyar Malaman Jami'o'i ta Najeriya (ASUU) ta yi barazanar shiga yajin aikin sai baba-ta-gani a jami'o'in jihohi 11 idan a ba a biya masu bukatunsu ba.

ASUU ta ce idan gwamnatocin jihohin Edo, Delta, Ondo, Adamawa, Borno, Taraba da Yobe ba su aiwatar da yarjejeniyar 2025 kafin karshen watan Yuli ba, za ta tsunduma yajin aiki.

Kara karanta wannan

Buba Galadima ya 'gano' shirin Tinubu da gwamnoni a kafa yan sandan jihohi

ASUU.
Tambarin kungiyar malaman jami'o'i ta Najeriya, ASUU Hoto: ASUU
Source: Twitter

Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa ASUU ta reshen Benin da reshen Yola ne suka bayyana hakan a tarukan manema labarai daban-daban da suka gudanar ranar Litinin.

Sun zargi gwamnatocin jihohin da rashin aiwatar da yarjejeniyar duk da cewa watanni shida sun shude tun bayan rattaba hannu a kanta.

ASUU ta fara shirin rufe jami'o'i 11

Shugaban ASUU na shiyyar Benin, Farfesa Monday Igbafen, ya ce rassan ASUU da ke jami'o'in da abin ya shafa sun fara shirya mambobinsu domin tsunduma cikin yajin aikin sai baba-ta-gani.

Jami'o'in da abin ya shafa sun hada da:

1. Jami'ar Ambrose Alli da ke Ekpoma, jihar Edo

2. Jami'ar Adekunle Ajasin da ke Akungba-Akoko, jihar Ondo

3. Jami'ar Kimiyya da Fasaha ta Olusegun Agagu, Okitipupa, jihar Ondo

4. Jami'ar jihar Delta da ke Abraka

5. Jami'ar Delta da ke garin Agbor

6. Jami'ar Dennis Osadebay da ke Asaba, jihar Delta

7. Southern Delta University, Ozoro

Kara karanta wannan

El Rufa'i: Dalilin kotu na ci gaba da fatali da bukatar belin tsohon gwamnan Kaduna

8. Jami'ar jihar Adamawa da ke Mubi

9. Jami'ar jihar Borno da ke Maiduguri

10. Jami'ar jihar Taraba da ke Jalingo

11. Jami'ar jihar Yobe da ke Damaturu

Dalilin barazanar kungiyar ASUU

Igbafen ya bayyana cewa yayin da jami'o'in gwamnatin tarayya da wasu jami'o'in jihohi suka aiwatar da yarjejeniyar, jihohin da abin ya shafa har yanzu ba su biya CATA da sauran alawus-alawus da aka amince da su ba.

A nasa bangaren, mai kula da ASUU a shiyyar Yola, Dani Mamman, ya ce ci gaba da kin aiwatar da yarjejeniyar da kuma biyan sauran hakkokin malamai ya jefa jami'o'in cikin yanayi na rashin kwanciyar hankali, in ji Daily Post.

Ambrose Alli
Tambari da harabar jami'ar Ambrose Alli da ke jihar Edo Hoto: Ambrose Alli University
Source: UGC

Ya bayyana lamarin a matsayin rashin adalci da kuma karya ka'idojin tattaunawar ma'aikata da gwamnati, yana mai cewa malamai ba sa neman wani abu da ya wuce hakkokinsu na doka.

ASUU ta yi kira ga gwamnonin jihohin da abin ya shafa da su gaggauta aiwatar da yarjejeniyar tare da biyan dukkan basussukan da ake bin su domin kauce wa shiga yajin aikin sai baba-ta-gani.

Kara karanta wannan

Abin da sabuwar dokar kafa 'yan sandan jihohi a Najeriya ta kunsa

ASUU ta cimma matsaya da gwamnati

A baya, kun ji cewa ƙungiyar ASUU da Gwamnatin Tarayya sun cimma matsaya kan sabunta yarjejeniyar shekarar 2009 bayan doguwar tattaunawa.

ASUU ta ce sabuwar yarjejeniyar za ta fara aiki ne daga 1, Janairu, 2026, kuma an tsara sake duba ta a duk bayan shekaru uku.

Yarjejeniyar ta mayar da hankali sosai kan walwalar malaman jami’o’i, inda aka amince da karin albashi kashi 40 cikin 100 ga dukkan ma’aikata masu koyarwa.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262