'Yan Ta'adda Sun Kutsa Makaranta a Borno, an Sace Daliban da Ke Zana Jarabawa

'Yan Ta'adda Sun Kutsa Makaranta a Borno, an Sace Daliban da Ke Zana Jarabawa

Jihar Borno - 'Yan ta'adda da ke ɗauke da makamai sun yi garkuwa da adadin ɗaliban da ba a kayyade ba a wata makarantar sakandare a jihar Borno.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

'Yan ta'addan sun sace daliban ne a makarantar sakandaren gwamnati ta jeka ka dawo da ke garin Lassa, a yankin karamar hukumar Askira/Uba a jihar Borno.

An sace dalibai a jihar Borno
Taswirar jihar Borno, tarayyar Najeriya Hoto: Legit.ng
Source: Original

Jaridar The Cable ta kawo rahoton cewa maharan sun afkawa makarantar ne a safiyar ranar Litinin, 29 ga watan Yunin 2026.

Maharan sun kai harin ne yayin da ɗalibai ke tsaka da zama domin rubuta jarabawar kammala sakandare ta Senior School Certificate Examination (SSCE) wadda hukumar jarabawa ta kasa (NECO) ke shiryawa.

An ruwaito cewa an kashe ɗaya daga cikin malamai lokacin da lamarin ya auku, yayin da wani na daban ya samu raunuka.

Nahum Daso, jami'in yaɗa labarai na rundunar 'yan sandan jihar Borno, ya tabbatar da aukuwar lamarin, inda ya ƙara da cewa wasu ɗalibai har yanzu ba a gano inda suke ba.

Ku dakaci karin bayani......

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng