Dama Ta Samu: Gwamnan Sokoto Ya Yi Sababbin Nade Nade a Gwamnatinsa
- Gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Ahmed Aliyu, ya zakulo wasu mutane domin shigar da su cikin gwamnati ta hanyar ba su mukaman da za a rika damawa da su
- Alhaji Ahmed Aliyu Sokoto ya nada masu bada shawara na musamman, manyan mataimaka na musamman da manyan sakatarori a gwamnatinsa
- A cikin sanarwar da mai magana da yawun bakin gwamnan ya fitar, an bayyana cewa nade-naden za su fara aiki ne nan take ba tare da bata lokaci ba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi
Jihar Sokoto, tarayyar Najeriya - Gwamnan jihar Sokoto, Alhaji Ahmed Aliyu, ya yi sababbin nade-nade na wasu mukamai a gwamnatinsa.
Gwamna Ahmed Aliyu ya amince da naɗin masu bada shawara na musamman, manyan mataimaka na musamman, manyan sakatarori da kuma mukaddashin babban sakatare.

Source: Facebook
Gwamna Ahmed ya yi nade-naden mukamai

Kara karanta wannan
"Kafin lokaci ya kure"; Yaron Gwamna Bala ya rubuta budaddiyar wasika ga mahaifinsa
An sanar da waɗannan naɗe-naɗe ne a cikin wata sanarwa da darakta janar na yaɗa labarai da hulɗa da jama'a na gidan gwamnatin Sokoto, Abubakar Bawa, ya fitar ranar Alhamis, 25 ga watan Yunin shekarar 2026 a shafin yanar gizo na gwamnatin jihar.
Gwamnan ya nada masu ba da shawara na musamman guda shida, manyan mataimaka na musamman guda uku, manyan sakatarori guda huɗu, da kuma mukaddashin babban sakatare guda ɗaya.
An yi nade-nade a gwamnatin Sokoto
Bisa ga sanarwar, sababbin masu bada shawara na musamman da aka naɗa su ne Garba Muhammad S/Birni, Mukhtari Bello Abdurrahman, Shi’itu M. Bello, Alhaji Tukur Sanyinna, Alhaji Abdullahi Jabo, da kuma Mamman Aliyu Salisu.
Gwamnan ya kuma naɗa Jummai Bello Kware, Nana Mamman Nasarawa, da kuma Hon. Emmanuel Ekereke a matsayin manyan mataimaka na musamman.
Haka zalika, an naɗa Buhari Umar, Abdullahi B. Muhammad, Musa Muhammad, da Jibril Sa’adu a matsayin manyan sakatarori, yayin da aka sanya sunan Aliyu Magaji a matsayin mukaddashin babban sakatare.
Sanarwar ta kuma bayyana cewa dukkan naɗe-naɗen za su su fara aiki ne nan take ba tare da bata lokaci ba.
Jerin sunayen waɗanda aka naɗa:

Kara karanta wannan
'Kashi 80 na matsalolin tsaro da suka addabi Sakkwato na da alaka da miyagun kwayoyi'
Masu bada shawara na musamman
Garba Muhammad S/Birni
Mukhtari Bello Abdulrahman
Shi’itu M. Bello
Alh. Tukur Sanyinna
Alh. Abdullahi Jabo
Mamman Aliyu Salisu
Manyan mataimaka na musamman
Jummai Bello Kware
Nana Mamman Nasarawa
Hon. Emmanuel Ekereke
Manyan sakatarori
Buhari Umar
Abdullahi B. Muhammad
Musa Muhammad
Jibril Sa’adu
Mukaddashin babban sakatare
Aliyu Magaji

Source: Facebook
Gwamnan Sokoto ya yi maganar rashin tsaro
A wani labarin kuma, kun ji cewa gwamnan jihar Sokoto, Ahmed Aliyu, ya bayyana alakar da ke tsakanin matsalar rashin tsaro da shaye-shayen miyagun kwayoyi.
Ahmed Aliyu, ya bayyana cewa kusan kashi 80 cikin 100 na matsalolin tsaron da jihar ke fuskanta na da nasaba da shaye-shayen miyagun kwayoyi da ake yi.
Gwamna Ahmed Aliyu ya bayyana cewa annobar shaye-shayen miyagun kwayoyi na daga cikin manyan barazanar da ke fuskantar makomar matasa da ci gaban al’umma.
Asali: Legit.ng