Hadimin Gwamna Ya Yi Murabus kan Rashin Samun Albashi na Tsawon Shekara
- Mai taimakawa gwamnan Benue kan harkokin matasa da yaɗa labarai ya yi murabus kan matsalar rashin albashi
- Bayan murabus ɗinsa, Atu Joseph ya yi zargin cewa ya yi aiki tsawon watanni ba tare da karɓar albashi ko alawus ba
- Murabus din nasa ya haifar da hasashen sauya sheƙar siyasa, musamman bayan ziyararsa ga George Akume kafin murabus ɗin
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Makurdi, Benue - Hadimi na musamman ga gwamnan Benue, Alia Hyacinth kan harkokin matasa da yaɗa labarai, Atu Terver Joseph, ya yi murabus.
Joseph ya yi murabus daga muƙaminsa ba tare da bata lokaci ba, yana mai bayyana cewa ya ɗauki matakin ne saboda dalilai na ƙashin kansa.

Source: Twitter
A cikin wasiƙar murabus da ya aikewa Sakataren Gwamnatin Benue, Atu ya gode wa Gwamna Hyacinth Alia bisa damar da aka ba shi ta yin aiki a gwamnatinsa, cewar Leadership.

Kara karanta wannan
'Tinubu ya dawo da zaman lafiya a wasu yankuna': Matawalle ya hango nasara a 2027
Tsohon hadimin gwamna ya godewa mai gidansa
Joseph ya godewa gwamnan bisa damarmaki da ya ba shi inda ya ce ya samu kwarewa ta fannoni da dama.
Ya ce:
"Cikin girmamawa da godiya nake miƙa murabus daga muƙamina na Mataimaki na Musamman ga Gwamna kan harkokin matasa da yaɗa labarai, wanda zai fara aiki nan take."
Ya ƙara da cewa yana matuƙar godiya da damar yin aiki ƙarƙashin gwamnatin Alia, tare da yaba masa saboda amincewar da ya nuna masa.
Atu ya ce ya samu ƙwarewa mai yawa yayin gudanar da aikinsa, sannan ya yi wa gwamnan fatan samun nasara a ci gaba da hidimtawa al'ummar Benue.
Sai dai bayan murabus ɗin, tsohon hadimin ya fitar da saƙon bidiyo inda ya yi zargin cewa ya yi shekara ta farko a aikinsa ba tare da karɓar albashi ko alawus ba.
Ya ce:
"Na yi aiki a shekara ta farko bayan wannan naɗi ba tare da albashi da alawus ba, amma duk da haka na ci gaba."

Source: Original
Yadda hadimin gwamna ya sha wahala a Benue
A cewarsa, sai bayan cikar shekara guda da naɗinsa ne ya fara karɓar albashi daga gwamnatin da yake yi wa aiki, cewar rahoton TheCable.
Har ila yau, Atu ya yi nuni da yiwuwar sauya sheƙar siyasa, bayan ya bayyana cewa ya kai ziyara ga Sakataren Gwamnatin Tarayya, George Akume, kafin murabus ɗinsa.
Wannan lamari ya jawo hasashe daga masu sa ido kan siyasa cewa tsohon mataimakin na iya sauya sansanin siyasa bayan ficewarsa daga gwamnatin Alia.
Koƙarin jin ta bakin Babban Sakataren Yaɗa Labaran Gwamnan, Sir Tersoo Kula, da Mai Ba da Shawara kan Yaɗa Labarai da Sadarwa, Cif Solomon Iorpev, bai yi nasara ba.
Gwamnan Benue zai ba manoma taki mai rahusa
A wani labarin, an ji cewa manoma za su samu taki a farashi mai rahusa bayan tallafin da gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia, domin gudanar da noma.
Gwanna Hyacinth Alia ya rage farashin takin zamani ga manoma inda a yanzu za su biya N28,000 kan kowane buhu.
Ya bukaci mutanen da za su jagoranci aikin da su gudanar da shi cikin gaskiya da rikon amana ba tare da karkatar da shi ba.
Asali: Legit.ng

