Kamfanin Airtel Ya Bi Sahun MTN, Ya Fara Tura wa Mutane Kudi a Wayoyinsu a Najeriya
- Kamfanin Airtel ya fara raba wa mutane katin waya a matsayin diyyar tangardar sabis da aka fuskanta tsakanin watan Nuwamba, 2025 zuwa Janairu, 2026
- Wannan mataki na zuwa ne bayan hukumar NCC ta umarci kamfanonin su biya abokan huldarsu diyyar rashin ingancin Intanet
- Tuni dai kamfanin MTN ya tura wa mutane katin waya zuwa cikin layukansu, yayin da Airtel ya biyo bayansa a 'yan kwanakin nan
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Abuja, Nigeria - Kamfanin sadarwa na Airtel Nigeria ya fara biyan 'yan Najeriya diyyar matsalar sabis da suka fuskanta a tsakanin watan Nuwamba, 2025 zuwa Janairu, 2026.
Hakan na zuwa ne bayan hukumar sadarwa ta kasa (NCC) ta umarci kamfanonin sadarwa a Najeriya sun fara bai wa masu amfani da layukansu diyya sakamakon matsalolin sadarwa.

Source: Instagram
Kamfanin Airtel ya bi umarnin NCC
Jaridar Leadership ta tattaro cewa kamfanin Airtel ya fara bin wannan umarni na hukumar NCC duk da cewa har yanzu miliyoyin mutane na fama da matsalolin intanet da kira a kasar nan
Wannan mataki na zuwa ne a matsayin wani sabon yunƙuri na gwamnatin Najeriya na gyara fannin sadarwa da aka dade ana suka saboda matsalolin yankewar kira, jinkirin intanet da rashin ingancin sabis.
Bincike ya nuna cewa manyan kamfanoni kamar Airtel da MTN Nigeria sun fara tura wa abokan huldarsu katin waya ta layukansu a matssyin diyyar matsalolin sabis da aka fudkanta tsakanin Nuwamba 2025 da Janairu 2026.
An kuma bukaci masu amfani da Airtel da su duba asusun layinsu ta wasu lambobin USSD, yayin da masu amfani da MTN suka tabbatar da karbar sakonnin biyansu diyya.
Adadin katin da Airtel ke turawa
Duk da haka, an gano cewa kudin diyya da kamfanonin ke tura wa mutane bai da yawa, inda wasu ke ganin an ba su N20 zuwa N600, gwargwadon girman matsalar da aka fuskanta a yanki.
Hukumar NCC ta bayyana cewa ba mayar wa mutane da kudindu aka yi ba, illa dai diyya ce da aka tanada saboda kamfanonin sun kasa cika ka’idojin ingancin sabis, cewar rahoton The Cable.
Dalilin NCC na daukar mataki
Shugaban hukumar NCC, Aminu Maida, ya ce matakin wani bangare ne na kokarin kare hakkin masu amfani da layukan sadarwa da kuma tilasta bin ka’idoji ga kamfanonin sadarwa.
Duk da wannan mataki, masana sun ce hakan bai warware matsalolin ba, kamar karancin kayan more rayuwa, tsadar aiki da kuma karuwar bukatar intanet.

Source: Twitter
Wani masani kan harkar fasahar sadarwa, Teju Abolade, ya ce ba tare da karin zuba jari da inganta sabis ba, wannan diyya ba zai zama mafita mai dorewa ba.
Ya kara da cewa inganta sadarwa na da matukar muhimmanci ga hada-hadar kudi, kasuwancin yanar gizo da bunkasar tattalin arzikin zamani a Najeriya.
MTN ya biya yan Najeriya diyya
A wani rahoton, kun ji cewa kamfanin MTN ya rabawa mutane katin waya a layukansu domin biyan diyyar matsalar sabis da aka samu a watan Janairu, 2026.
Masu amfani da layukan MTN a Najeriya da dama sun tabbatar da cewa sun samu sakon katin waya a wayoyinsu,
Masu amfani da layukan MTN sun tabbatar da cewa kudin da aka tura ya bambanta, ba adadi daya aka tura wa kowa ba, inda aka tura wa wasu katin N20, wasu N91, yayin da wasu kuma suka samu har N341.
Asali: Legit.ng

