Neja da Jihohin Arewa 10 Za Su Fuskanci Iska Mai ƙarfi da Ruwan Sama Gobe Juma'a

Neja da Jihohin Arewa 10 Za Su Fuskanci Iska Mai ƙarfi da Ruwan Sama Gobe Juma'a

  • Hukumar NiMet ta yi hasashen cewa za a samu yanayin zafi da rana a gobe Juma'a, amma za a samu ruwan sama da iska a wasu jihohin Arewa
  • Wasu jihohin Arewa da Kudancin ƙasar za su fuskanci iska mai karfi da kuma ruwan sama mai yawa, tun daga safiya har zuwa yammacin ranar
  • NiMet ta buƙaci matafiya da direbobi da su kasance masu taka-tsantsan yayin tuki domin guje wa haɗurran da santsin titi ke yawan haddasawa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Sani yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Abuja – Hukumar kula da yanayi ta ƙasa (NiMet) ta fitar da hasashen yanayi na ranar Juma'a, 17 ga watan Afrilu, 2026, inda ta ce akwai yiwuwar samun iska mai karfi da ruwan sama a sassa daban-daban na ƙasar.

Hukumar ta buƙaci ƴan Najeriya da su kasance cikin shiri domin kiyaye afkuwar haɗurra sakamakon sauyin yanayin da za a fuskanta.

Kara karanta wannan

Yakin Iran, Amurka: Najeriya da wasu kasashe na iya samun tallafin dala biliyan 50

Yanayin Arewa Da Tsakiyar Najeriya

A yankin Arewa, ana ran samun yanayin zafi da rana tare da gajimare a wasu wurare da safe, amma ana sa ran samun ruwan sama da aradu a jihar Taraba. Daga baya da yamma, ana sa ran ruwa mai matsakaicin ƙarfi zai mamaye jihohin Bauchi, Gombe, Kaduna, Adamawa, da kuma Taraba. Wannan na nufin za a fuskanci iska mai ƙarfi da walƙiya a waɗannan yankuna masu zafi.

A yankin Tsakiya kuwa, za a tashi da gajimare da safe musamman a jihohin Neja da Nasarawa. Zuwa yamma, ana sa ran samun ruwan sama a kusan dukkan jihohin yankin da suka haɗa da Kwara, Benue, Plateau, Kogi, da kuma babban birnin tarayya Abuja. NiMet ta ba da shawarar mutane su tsara ayyukansu na waje da wuri domin guje wa ruwan yamma.

Kudancin Najeriya Da Gargaɗin Tsaro

Yankunan Kudancin Najeriya za su kasance cikin yanayin gajimare tun da safe, tare da yiwuwar samun ruwan sama a jihohin Rivers, Bayelsa, Cross River, da Akwa Ibom. Zuwa yamma, ruwan saman zai bazu zuwa kusan dukkan jihohin yankin ciki har da Legas, Oyo, Edo, da Anambra. Wannan yanayi na iya kawo cikas ga zirga-zirga da ayyukan yau da kullum sakamakon walƙiya da jika hanyoyi.

Hukumar ta fitar da muhimman shawarwari ga jama'a kamar haka: mutane su kiyaye hanyoyin da ambaliya ke shafa yayin da ake ruwa. Direbobi su rage gudu sakamakon rashin gani sosai da kuma santsin hanya. A nemi wurin buya idan ana tsawa domin kariya daga harbin walƙiya. Sannan kamfanonin jiragen sama su rinka samun rahoton yanayi daga NiMet domin tabbatar da tsaron jirage yayin tashi ko sauka.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com