Isra'ila Za Ta Rufe Gidan Talabijin Na Aljazeera a Kasarta

Isra'ila Za Ta Rufe Gidan Talabijin Na Aljazeera a Kasarta

  • Yayin da ake ci gaba gumurzu a Isra'ila, gwamnatin kasar ta shirya rufe gidan talabijin na Aljazeera a ƙasar
  • Fira Ministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu shi ya tabbatar da haka inda ya ce za su kwace kayan aikinsu a kasar
  • Gwamnatin kasar na zargin gidan talabijin din da ke kasar Qatar da ruruta wutar rikicin da goyon bayan Hamas

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Isra'ila - Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu ya ce gwamnatinsa za ta rufe gidan talabijin na Aljazeera.

Netanyahu ya zargi gidan talabijin din na kasar Qatar da kara ruruta wutar rikici a kasar Isra'ila wurin goyon bayan Hamas.

Isra'ila za ta rufe gidan talabijin na Aljazeera
Fira Ministan Isra'ila ya ce za su rufe gidan talabijin na alhazai. Hoto: @netanyahu.
Asali: Twitter

Wane mataki Isra'ila ta dauka kan Aljazeera?

Kara karanta wannan

'Akwai manyan da ke yi wa gwamnatina makarkashiya', Gwamnan APC ya koka

Fira Ministan ya bayyana haka ne a yau a shafinsa na X inda ya ce zai kawo karshen matsalar da suke da Ita.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

"Gwamnati ta amince da rufe tashar Aljazeera da ke ruruta wutar rikici a Isra'ila."

- Benjamin Netanyahu

Netanyahu ya ce wakilan Aljazeera sun kara lalata tsaron kasar inda ya ce lokaci ya yi da ya kamata a rusa masu goyon bayan Hamas a cikin kasar.

Isra'ila ta zargi Aljazeera da son Hamas

Har ila yau, Ministan Sadarwa a Isra'ila, Shlomo Karhi shi ma ya bayyana goyon bayansa kan daukar matakin.

Shlomo ya ce babu wani 'yancin fadan albarkacin baki ga masu goyon bayan Hamas a rikicin Isra'ila.

"Babu batun 'yancin fadan albarkacin baki ga wadanda ke yabon Hamas a Isra'ila."
"Za mu rufe Aljazeera da gaggawa kuma za mu kwace dukkan kayayyakinsu."

Kara karanta wannan

Gwamnati za ta dawo da lantarki a garuruwan da aka yi shekaru babu wuta a Sokoto

- Shlomo Karhi

Turkiyya ta yanke alaka da Isra'ila

Kun ji cewa shugaban kasar Turkiyya, Recep Erdogan, ya sanar da dakatar da harkokin kasuwanci da kasar Isra'ila.

Ma'aikatar kasuwanci ta kasar ta ce daukan matakin yana da alaka da musgunawa Falasɗinawa da Isra'ila ke yi.

Kasar Turkiyya dama ta kasance cikin jerin ƙasashen da suke nuna wa Isra'ila yatsa tun fara kai hare-haren da ta yi zuwa Gaza a watan Oktoban shekarar 2023.

Asali: Legit.ng

Online view pixel