Babu Wanda Zai Hana: NLC Ta Nemi Bukata 1 Daga Gwamnati Wajen Shirya Zanga Zanga

Babu Wanda Zai Hana: NLC Ta Nemi Bukata 1 Daga Gwamnati Wajen Shirya Zanga Zanga

  • Shugabannin NLC ba su yarda su fasa yi zanga-zangar lumuna ba duk da taron da aka yi domin gwamnatin tarayya ta lallashe su
  • Sakataren gwamnatin tarayya, Ministoci da DG DSS sun zauna da wakilan NLC da TUC da sauran kungiyoyin ‘yan kasuwa da ma’aikata
  • An tashi taron ba tare da an yi wata nasara ba, shugaban kungiyar NLC ya bukaci gwamnati ta ba su kariya wajen zanga-zangarsu

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.

Abuja - Gwamnatin tarayya ba ta iya shawo kan kungiyar ‘yan kwadago ta kasa watau NLC ta fasa shirya zanga-zangarta ba.

Duk da an zauna da manyan jami’an gwamnati, The Cable ta ce shugabannin ma’aikatan sun cije sai sun cigaba da zanga-zanga.

Kara karanta wannan

NLC ta yi bazaranar ɗaukar mataki 1 idan aka farmaki masu zanga-zangar lumana a ƙasar

Zanga-zanga
NLC za ta cigaba da zanga-zanga Hoto: Getty Images/Buhari Sallau
Asali: UGC

Zanga-zanga: SGF ya hadu da 'yan kwadago

Sakataren gwamnatin tarayya watau George Akume ya jagoranci wakilan gwamnati domin a zauna da manyan ‘yan kwadago.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Shugabannin NLC da TUC ta ‘yan kasuwa da sauran ma’aikatan Najeriya sun halarci zaman duk da TUC ba ta cikin zanga-zangar.

Matsayar NLC a kan zangar-zangar lumuna

A karshen taron da aka yi, Joe Ajaero wanda shi ne shugaban NLC, ya shaida cewa ba za su fasa yin zanga-zangar lumunar nan ba.

An rahoto Joe Ajaero yana cewa za su yi zanga-zangar gama-garin ne domin nuna rashin jin dadinsu a kan matsin tattalin arziki.

Ana bukatar tsaro wajen zanga-zanga

Jagoran ya shaidawa ‘yan jarida hakki ya rataya a wuyan kowane bangare wajen ganin an yi zanga-zangar ba tare da rikici ba.

Kara karanta wannan

‘Yan kwadago sun yanke matsaya kan hakura da zanga-zanga saboda barazanar DSS

Shugaban kungiyar NLC ya bukaci gwamnatin tarayya ta ba su jami’an tsaro kamar yadda tsari da dokar kasa suka bada dama.

"Za a yi zanga-zangar kuma nauyi ne a tsarin mulki a wuyansu (gwamnati) domin tabbatar da cewa an yi zanga-zangar lafiya"
"Muna da bukatun da dole mu gabatar, saboda haka watakila gobe (Talata) idan mun gabatar da bukatun, ‘yan jarida za su samu takardar.”

- Joe Ajaero

Daily Trust ta ce an yi zaman ne da Ministocin noma, kasafi, kwadago, shari’a, shugabar ma’aikata da kuma Darekta Janar na DSS.

ASUU za ta shiga zanga-zangar NLC

Legit ta ji labari kungiyar malaman jami’a watau ASUU ta reshen ABU Zariya ta fitar da sanarwa cewa za ta shiga zanga-zangar nan.

Kwanaki da biyan malaman jami’ar, sai ga 'yan ASUU suna goyon bayan kungiyar NLC wajen kokawa da tsadar rayuwar da aka shiga.

Asali: Legit.ng

Online view pixel