Oronsaye: Wasu Ma’aikatu da Hukumomi 45 da Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Rusawa

Oronsaye: Wasu Ma’aikatu da Hukumomi 45 da Gwamnatin Tarayya Za Ta Iya Rusawa

  • Bola Ahmed Tinubu ya bada umarni a dabbaka shawarwarin da kwamitin Steve Oronsaye ya ba gwamnatin Goodluck Jonathan
  • Sabon shugaban Najeriyan ya dauki wannan mataki ne a wajen zaman majalisar FEC da aka yi domin rage kashe kudi a kasar
  • An nemi hada NEMA da sauran hukumomin da ke kula da ‘yan gudun hijira a Najeriya, akwai hukumomi 30 da za a iya soke su

Abuja - Tsohon shugaban ma’aikatan gwamnatin tarayya ya kawo shawarar a soke wasu ma’ikatu, ya kuma nemi a dunkule wasunsu.

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince a aiwatar da shawarar Steve Oronsaye a gwamnatin tarayya bayan an yi watsi da aikin.

Oronsaye - Asiwaju Bola Ahmed Tinubu
Shugaban kasa Bola zai yi aiki da shawarar Oronsaye a Najeriya Hoto: @OfficialABAT
Asali: Twitter

Gwamnatin Tinubu za ta rage kashe kudi

Matakin ya zo ne jim kadan bayan Atiku Abubakar ya bada irin wannan shawara, ya ce Bola Tinubu ya yi koyi da shugaban Argentina.

Kara karanta wannan

Ma'aikata za su rasa ayyukansu, Shehu Sani ya yi martani kan amincewa da rahoton Oronsaye

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Legit ta dubi shawarwarin da kwamitin Steve Oronsaye ya gabatar mai shafi 90, ta duba hukumomi da ma’aikatan da za a iya rusawa.

A lokacin da aka yi aikin nan, ma’aikatu da cibiyoyi 541 ake da su a tarayya, zuwa yanzu an kirkiro wasu sababbi kamar NDPB a 2022.

Aikin Oronsaye zai tashi kujerun hajji?

NCNE da UBEC za su koma hukuma daya kamar yadda za a yi wa NASENI da wata ma’aikata, watakila a gwama NCAC da wasunta.

Hukumomin NAHCON da NCPC za su tashi aiki, hakan yana nufin babu ruwan gwamnati da harkar alhazai da masu ziyarar kirista.

NTA, FRCN da VON duka za su shiga wata hukuma mai alhakin watsa labarai. AFIT da jami’ar sojoji za su zama ‘yaruwar makarantar NDA.

Sauran shawarwarin kwamitin Oronsaye

An bada shawarar ruguza FRC da NSIWC, a bar aikinsu a hannun RMAFC sai a hada CCB, EFCC da ICPC a cikin wata hukuma guda dabam.

Kara karanta wannan

Babban labari: Tinubu ya shirya amfani da rahoton Oronsaye, zai yi wani babban sauyi a Najeriya

NIPOST, NCC, NBC za su zama hukuma daya idan aka yi amfani da shawarar Oronsaye, sai canjin suna da aka yi wa CCB da FCSC.

Jerin ma'aikatun da za a soke ko su narke

1. FRC

2. FAAN

3. NSIWC,

4. CCB

5. EFCC

6. ICPC

7. PCC

8. NACA

9. NEMA

10. PCC

11. NACA

12. ICRC

13. NCAA

14. NOSDRA

15. NESREA

16. OGFZA

17. FERMA

18. NIPC

19. NCNE

20. NCAC

21. NASENI

22. FIIRO

23. PRODA

24. BCDA

25. RMRDC

26. NABDA

27. NNMDA

28. NAHCON

29. NCPC

30. NCC

31. NBC

32. NITDA

33. ECN

34. NIPOST

35. NALDA

36. NIDCOM

37. NCMM

38. DMO

39. NAPEP

40. PSIN

41. ASCON

42. NCDMB

43. NGSA

44. FAAN

45. UCC

CBN: 'Yan canji sun tsorata da Tinubu

‘Yan kasuwar canji musamman daga Arewa sun tsorata da sababbin ka’idojin da CBN ya fito da su, ana da labari suna ganin za a yake su ne.

Masu sana’ar saye da saida kudin ketare sun zargi Yemi Cordoso da nemin ganin bayansu. Akwai wadanda suka yabi sababbin dokokin.

Asali: Legit.ng

Online view pixel