Wike Ya Fitar da Naira Biliyan 30.9 Don Yin Wani Babban Aiki a Abuja

Wike Ya Fitar da Naira Biliyan 30.9 Don Yin Wani Babban Aiki a Abuja

  • Nyesom Wike ya ba da umurnin fitar da naira biliyan 30.9 don yin gyara da sake fasalin wasu makarantu a Abuja
  • Wike zai kashe naira biliyan 13.3 don gyara makarantu 40, sai kuma naira biliyan 13.1 na sabunta makarantu 18
  • Akwai kuma naira biliyan 4.5 da ministan babban birnin tarayyar ya ware don yin aikin wasu makarantu hudu

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fanni n nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

FCT, Abuja - Ministan babban birnin tarayya (FCT) Nyesom Wike ya amince a fitar da naira biliyan 30.9 don gyara makarantu a Abuja.

Sakataren ilimi na FCT, Dokta Danlami Hayyo ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai jiya a Abuja.

Kara karanta wannan

Mai gadin makaranta a Kano ya dauki ransa a cikin aji saboda tsohuwar matarsa ta sake aure

Wike zai yi wa makarantun Abuja kwaskwarima, zai kashe naira biliyan 30.9
Wike zai yi wa makarantun Abuja kwaskwarima, zai kashe naira biliyan 30.9. Hoto: @GovWike
Asali: Facebook

Kudin da za a kashe akan kowacce makaranta

Dokta Danlami Hayyo ya ce amincewa da fitar da kudaden ya nuna fifikon da ministan ya ba wa bangaren ilimi, Leadership ta ruwaito.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hayyo ya ce, za a kashe naira biliyan 13.3 don gyara da farfado da makarantu 40, wadanda za a kammala aikin su nan da kwanaki 100.

Ya kara da cewa za kuma a kashe naira biliyan 13.1 don sabunta fasalin wasu makarantu gaba daya, wanda za a fara da makarantu 18.

Wadanne gyare-gyare za ayi a makarantun?

Sakataren ya ce an tsara sabunta komai na makarantun domin saka sabbin ababen more rayuwa da kayan aiki na zamani.

Abubuwan da za a gyara sun hada da bandaki, dakunan kwanan dalibai, cin abinci da samar da kujeru da ruwa.

Ya ce za a kuma gyara makarantu hudu a kashi na biyu na tsarin sabunta ginin makarantun gaba daya a kan kudi naira biliyan 4.5.

Kara karanta wannan

Nyesom Wike: Ana kukan tsadar rayuwa, Minista yayi karin kudin makarantu a Abuja

Jerin makarantun da za a yi wa kwaskwarima

  • Kwalejin kimiyya da fasaha ta Gwamnati, Kwali
  • Kwalejin kimiyya da fasaha ta Gwamnati, Maitama
  • Kwalejin kimiyya da fasaha ta Gwamnati, Kuje
  • Kwalejin kimiyya da fasaha ta Gwamnati, Wuse II

Ya ce dukkan ayyukan za a kammala su ne kafin watan Mayun 2024 kuma Shugaba Bola Tinubu zai kaddamar da su a bikin cika shekara guda a kan karagar mulki.

Hayyo ya yabawa ministan kan yadda ya magance matsalar da ta kunno kai tsakanin malaman firamare da sakatariyar kananan hukumomin yankin.

Binani Vs Fintiri: Kotun Koli ta yanke hukuncin zaben Adamawa

A wani labarin, Kotun Koli a ranar Laraba, ta yanke hukuncin karshe kan shari'ar zaben gwamnan jihar Adamawa.

Kotun ta ce Ahmadu Fintiri shi ne halastacce kuma zaɓaɓɓen gwamnan Adamawa ba wai A'isha Dahiru ba.

Asali: Legit.ng

Online view pixel