Farfesa Osinbajo Ya Samu Babban Mukami A Hukumar Yanayi Ta Afirka

Farfesa Osinbajo Ya Samu Babban Mukami A Hukumar Yanayi Ta Afirka

  • Farfesa Yemi Osinbajo ya samu babban mukami a Hukumar Yanayi a Nahiyar Afirka wanda zai jagoranta
  • Farfesan ya bayyana haka ne a shafinsa na Twitter a yau Laraba 27 ga watan Satumba inda ya ce ya yi matukar murna
  • Wannan shi ne mukami na biyu da tsohon mataimakin shugaban kasar ya samu bayan barinshi ofis a watan Mayu

DUBA NAN: Bibiyi shafin Legit.ng Hausa a kafar TikTok. Kada ka bari bidiyo mai daukar hankali ya wuce ka!

FCT, Abuja – Tsohon mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya samu mukami a hukumar Yanayi ta Afirka.

Osinbajo ya samu mukamin ne a matsayin shugaban Hukumar Yanayi ta Afirka (CAP-A), Legit ta tattaro.

Yemi Osinbajo ya sake samun sabon mukami
Farfesa Osinbajo Ya Sake Samu Babban Mukami. Hoto: Yemi Osinbajo.
Asali: Twitter

Wane mukami Osinbajo ya samu karo na biyu?

Farfesan ya bayyana haka ne a shafinsa na Twitter a yau Laraba 27 ga watan Satumba inda ya ce ya yi matukar murna da samun mukamin.

Kara karanta wannan

Shugabar Karamar Hukumar da Ya Zargi Gwamnan APC da Wawure Kuɗi Ya Shiga Sabuwar Matsala

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Ya rubuta kamar haka:

“Ina murnar samun wannan mukamin da na karba na jagorantar Hukumar Yanayi a Afirka (CAP-A), za mu kawo sauyi a bangaren yanayi da jajirtattun abokan aiki.

Wannan mukami na Osinbajo shi ne na biyu tun bayan barin ofishi a matsayin mataimakin shugaban kasa a ranar 29 ga watan Mayu.

Wane mukami Osinbajo ya fara samu?

A farkon watan Yuli, Osinbajo ya samu mukamin mai ba da shawara na musamman a hukmar makamashi da harkokin jama'a (GEAPP).

Hukumar ta sanar da mukamin nashi ne a ranar Talata 11 ga watan Yuli a yanar gizonta.

Farfesa Osinbajo ya kasance tsohon mataimakin shugaban kasa a mulkin Muhammadu Buhari na wa'adi biyu da su ka yi daga shekarar 2015 zuwa 2023.

Osinbajo shi ne ya ke jagorantar Kwamitin Tattalin Arziki (NEC) a lokacin gwamnatin tsohon shugaban kasa, Buhari.

Kara karanta wannan

Gwamnan APC Ya Yi Magana Mai Kyau Bayan Kotun Zabe Ta Yanke Hukunci Kan Nasarar Da Ya Samu a Zaɓen 2023

Ya kuma rike bangaren tsare-tsaren kudade da ba da tallafi na 'Trader Money' a lokacin da su ke kan mulki.

Osinbajo ya samu sabon mukami bayan barin ofis

A wani labarin, tsohon mataimakin shugaban kasa, Farfesa Yemi Osinbajo ya samu sabon mukami makwanni shida bayan barin ofis a watan Mayu.

Osinbajo ya samu mukamin ne a kamfanin Global Energy Alliance for People and Planet a matsayin mai ba da shawara na musamman.

Tsohon mataimakin shugaban kasar ya bayyana haka a ranar Talata 11 ga watan Yuli a shafinsa na Twitter.

Asali: Legit.ng

Online view pixel