Hukumar Zabe ta INEC Ta Ba Tinubu da Shettima Takaddun Shaidan Lashe Zaben Shugaban Kasa Na 2023

Hukumar Zabe ta INEC Ta Ba Tinubu da Shettima Takaddun Shaidan Lashe Zaben Shugaban Kasa Na 2023

  • Hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta mika takardun shaidan lashe zaben shugaban kasa ga Bola Ahmad Tinubu da Kashim Shettima na jam'iyyar APC
  • An tashi da rahotannin cewa, Bola Ahmad Tinubu ne ya lashe zaben shugaban kasa da aka yi a Najeriya a ranar 25 ga watan Faburairun 2023
  • Ya zuwa yanzu, jiga-jigan siyasa a Najeriya na ci gaba da mika sakon murna ga zababben shugaban kasan Najeriya Tinubu

FCT, Abuja - Hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta mikawa Bola Ahmad Tinubu, zababban shugaban kasa a Najeriya da mataimakinsa, Kashim Shettima takardun shaidar lashe zaben ranar 25 ga watan Faburairu.

Shugaban INEC, Mahmud Yakubu ne ya gabatarwa jiga-jigan siyasan biyu takardun a ranar Laraba 1 ga watan Maris da yamma a cibiyar manyan taruka ta kasa da ke Abuja, Punch ta ruwaito.

Kara karanta wannan

"Ba A Taba Yin Ingantaccen Zabe Na Gaskiya Kamar Na 2023 Ba A Najeriya", Kashim Shettima

Ba da takardun na zuwa ne jim kadan bayan da hukumar ta bayyana a gidajen talabijin na Najeriya cewa, Tinubu ya fi kowa yawan kuri'u a zaben na bana.

Tinubu ya karbi shaidar lashe zabe daga INEC
Zababben shugaban kasan Najeriya, Bola Tinubu | Hoto: dailypost.ng
Asali: UGC

Kuri'un da 'yan takara suka samu a zaben bana

Tinubu ne ya lashe zaben shugaban kasa da aka yi a Najeriya, inda ya samu kuri'u 8,794,726 a karkashin inuwar jam'iyyar APC.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

Atiku Abubakar na PDP ne ya zo na biyu a zaben, inda ya tattara yawan kuri'un da suka kai 6,984, 520 a zaben,

A bangare guda, Peter Obi ya zo na uku, inda ya samu kuri'u 6,101,533 a karkashin inuwar jam'iyyar Labour.

Sauran jam'iyyun siyasa sun samu rabonsu daga sauran kuri'un da aka kada a jihohin kasar baki daya a ranar Asabar da ga tabata.

A tun farko, hukumar zabe ta INEC ta ce za ta ba Tinubu da Shettima takardun ne a yau Laraba 1 ga watan Maris din 2023, kamar yadda RipplesNigeria ta ruwaito.

Kara karanta wannan

'Yan Najeriya sun yi dabara: Gwamnan APC na Arewa ya taya Tinubu murna, ya yiwa 'yan kasa jawabi

Buni ya taya Tinubu murnar lashe zabe

A wani labarin kuma, kun ji yadda gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya taya Tinubu murnar lashe zaben shugaban kasa.

A cewar Buni, Tinubu ne wanda ya fi cancanta ya gaji Buhari, kuma hakan ya tabbata ta hanyar yin zaben bana.

Ya yabawa 'yan Najeriya bisa jajircewa da amincewa da jam'iyyar a cikin irin wannan yanayi mai bukatar ujila.

Asali: Legit.ng

Online view pixel