Zo Ka Nemi Aiki: Dan Najeriya Ya Nemo Kamfanin da Ke Biyan Albashin Naira Miliyan 3 Duk Wata

Zo Ka Nemi Aiki: Dan Najeriya Ya Nemo Kamfanin da Ke Biyan Albashin Naira Miliyan 3 Duk Wata

  • Dan Najeriya ya fadi wasu ayyuka guda biyu da mutum zai iya nema wanda ke biyan naira miliyan uku duk wata
  • Kamfanonin dai na aiki ne a Abuja kuma suna neman kwararre da zai kama aiki a guraben da zai samu kudade masu yawa
  • Mutane da yawa sun karyata bayaninsa, sai dai jim kadan bayan da ya tura adireshin kamfanonin, an tabbatar da ikirarinsa

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza, kwararren edita ne a fannin nishadi, al'amuran yau da kullum da kuma siyasa. Yana da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Wani dan Najeriya ya wallafa a shafinsa na Twitter cewa akwai guraben aiki da za a biya albashin naira miliyan uku duk wata.

Mutumin mai amfani da sunan @3mbeeeee a Twitter ya bayyana cewa a Abuja ake yin aikin kuma kamfanonij na neman kwararru da za su kama aiki nan take.

Kara karanta wannan

Sabuwar zanga-zanga ta barke a Abuja kan kujerar Wike

Hotuna daga wuraren daukar aiki
Dan Najeriya ya gano wasu ayyuka biyu da ke biyan albashin naira miliyan uku duk wata. Hoto: Getty Inages A kula: Anyi amfani da hoton ne don nuna misali kawai
Asali: Getty Images

Sai dai da yawa ba su gamsu da wannan bayanin na sa ba, inda daga bisani ya wallafa adireshin neman aikin don tabbatarwa.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Jaridar Legit ta tattaro cewa kamfanin na neman kwararru a fannin 'warware rikici' da kuma 'mawallafi kan kyawun halittu'

Ana iya samun karin bayanai kan ayyukan anan da nan.

Duba wallafarsa a kasa:

Ma'aikatan tarayya 2,000 sun rasa albashin watan Nuwamba

A wani labarin, kun karanta cewa akalla ma'aikatan gwamnatin tarayya dubu biyu ne suka rasa albashin su na watan Nuwamba, kamar yadda majiya mai tushe ta bayyana hakan a ranar Litinin.

Wani ma'aikaci gwamnati a ma'aikatar tsaro ta kasa, ya yi nuni da cewa da yawa daga cikin ma'aikatan da ke aiki a ma'aikatar ba su samu albashin su ba, Legit Hausa ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Kotu ta garkame lebura wata 7 a gidan gyaran hali kan satar agwagi guda 3 a Filato

Ma'aikacin gwamnatin ya kuma yi nuni da cewa gaza samun albashin ba zai rasa nasaba da tantancewa da ofishin shugaban ma'aikatan tarayya da ke yi a kasar ba.

Da gaske gwamnati ta yi gwanjon babban otel mallakin jihar Kwara?

A wani labarin na daban, a yayin da ake ci gaba da yada jita-jitar cewa an cefanar da babban otel mallakin jihar Kwara, gwamnatin jihar ta fito ta yi martani akai.

Gwamnatin jihar ta ce babu wani dalili da zai saka a sayar da otel din, kawai ta yi gwanjon kayan cikinsa ne don yin gyare-gyare.

Asali: Legit.ng

Online view pixel