Wuta Ta Yi Wuta: An Kai Hare Hare Masu Zafi a Biranen Saudiyya

Wuta Ta Yi Wuta: An Kai Hare Hare Masu Zafi a Biranen Saudiyya

  • Ƙungiyar Houthi ta kai hari kan biranen Khamis Mushait, Abha da Jizan na Saudi Arabiya da makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa
  • Hare-haren da aka kai a baya sun jikkata mutane 73 tare da haddasa gobara a wasu cibiyoyin samar da mai
  • Ƙaruwar faɗa tsakanin Saudiyya da Houthi na ƙara fargabar sake komawa ga yaƙin da aka dakatar da shi tun bayan tsagaita wuta ta 2022

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Birnin Jeddah, Saudiyya - Rundunar hadin gwiwa da Saudiyya ke jagoranta da ke yaƙi da Houthi a Yemen ta ce mayakan ƙungiyar sun kai hari kan birane uku na Saudiyya.

Rundunar ta bayyana cewa mayakan Houthi sun kai hare-haren ne a biranen Khamis Mushait, Abha da Jizan da makamai masu linzami da jirage marasa matuƙa.

Mayakan Houthi sun kai hari a Saudiyya
Wuta ta kama a matatar Saudi Aramco bayan kai hari Hoto: AFP via Getty Images
Source: Getty Images

Tashar Aljazeera ta kawo rahoton cewa mai magana da yawun rundunar hadin gwiwar ya bayyana hakan cikin wata sanarwa a ranar Laraba, 9 ga watan Satumban 2026.

Kara karanta wannan

Ana tsaka da yakin Iran, ƙasar Saudiyya ta kai munanan hare hare kan manyan birane 3

Ya ce mayakan Houthi na ci gaba da kai hare-haren da suka shafi kadarorin ƙasar da muhimman ababen more rayuwa na Saudiyya.

“Mayakan Houthi na ci gaba da kai munanan hare-hare kan kadarorin ƙasa da ababen more rayuwa na masarautar,” in ji sanarwar.

An yi gargadin yiwuwar haɗari

A safiyar ranar Laraba, Hukumar Kare Fararen Hula ta Saudiyya ta gargadi jama’a a lardin Khamis Mushait da birnin Abha kan yiwuwar fuskantar haɗari.

Daga baya hukumar ta ɗage wani gargaɗin da ta bayar a Khamis Mushait, kwana guda bayan hare-haren Houthi a birnin da wasu birane uku da ke kusa, cewar rahoton tashar Reuters.

Hare-haren sun jikkata mutane 73 tare da haddasa gobara a wasu cibiyoyin man fetur, kamar yadda rahotanni suka bayyana.

Mayakan Houthi sun kai hari Saudiyya

A ranar Talata, mayakan Houthi da ke samun goyon bayan Iran sun kai hari kan wani sansanin sojojin sama a Khamis Mushait da kuma wasu cibiyoyin samar da mai a biranen da ke kusa.

Kara karanta wannan

Dan takara ya yi alkawarin samar da lantarki a kowane gida cikin watanni 11 a Najeriya

An bayyana harin a matsayin ɗaya daga cikin manyan hare-haren da aka kai a Saudiyya tun bayan fara yaƙin da Amurka da Isra’ila suka yi wa Iran a watan Fabrairun 2026.

Mahukuntan Saudiyya ba su bayyana dalilin da ya sa aka bayar da sabon gargaɗin a Khamis Mushait ranar Laraba ba.

Tsoron sake komawa yaƙi

Yaƙin da ke tsakanin Saudiyya da mayakn Houthi ya ƙara tsananta a cikin watannin baya-bayan nan, lamarin da ya haifar da fargabar sake komawa wani yaƙi mai girma.

A shekarar 2022, tsagaita wuta da Majalisar Ɗinkin Duniya ta taimaka wajen cimmawa ta rage yaƙe-yaƙen da suka shafe shekaru ana yi a Yemen.

Saudiyya ce ke jagorantar wata rundunar hadin gwiwar ƙasashen Larabawa da ke goyon bayan gwamnatin Yemen mai hedikwata a kudancin ƙasar.

Gwamnatin ta bar babban birnin Yemen, Sanaa, bayan da mayakan Houthi suka ƙwace birnin daga hannunta shekaru 12 da suka gabata.

Houthi ta kai hari Saudiyya
Mai magana da yawun kungiyar Houthi, Yahya Saree Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Saudiya ta kai hare-hare a Yemen

A wani labarin kuma, kun ji cewa jiragen yakin Saudiya na kai hare-haren sama a wasu larduna daban-daban na kasar Yemen.

Hare-haren sun shafi lardunan Marib, al-Jawf da Taiz, inda aka ruwaito cewa Saudiyya ta yi luguden wuta a yankin Khab wa Sha'af da ke lardin al-Jawf.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng