Wata Sabuwa: Babban Yaron Netanyahu Ya Burma cikin Matsala a Amurka

Wata Sabuwa: Babban Yaron Netanyahu Ya Burma cikin Matsala a Amurka

  • An gaggauta mayar da Yair Netanyahu, babban ɗan Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, daga Amurka zuwa Isra’ila
  • Hukumar leƙen asirin cikin gida ta Isra’ila, Shin Bet, ta ce an yi hakan ne bayan tantance girman barazanar da ke fuskantar Yair
  • Rahotanni sun ce a baya an zargi Iran da shirya kashe Yair a Florida, inda ya shafe shekaru yana zaune

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

​​​​​​​​​​​​​​Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da kwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishadi

Birnin Tel Aviv, Israila - An gaggauta mayar da Yair Netanyahu, babban ɗan Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu, daga Amurka zuwa Isra’ila.

An mayar da babban yaron na Netanyahu zuwa Israila ne bayan hukumar leƙen asirin cikin gida ta ƙasar ta gano wata barazana ga rayuwarsa.

Yair Netanyahu ya bar Amurka cikin gaggawa
Yair Netanyahu tare da mahaifinsa Benjamin Netanyahu Hoto: THOMAS COEX
Source: Getty Images

Tashar Aljazeera ta kawo rahoton cewa hukumar Shin Bet ta bayyana a cikin wata sanarwa da ta fitar a yammacin Asabar, 29 ga watan Agustan 2026.

Kara karanta wannan

Abin tausayi: 'Yan mata 'yan gida daya sun rasu a hatsarin kwale kwale a Kano

Hukumar ta bayyana cewa an samu “babbar barazana ta cutar da Yair Netanyahu”, lamarin da ya sa aka yanke shawarar dauke shi cikin gaggawa tare da tawagar tsaron da ke tare da shi zuwa Isra’ila.

Sai dai hukumar ba ta bayyana inda barazanar ta fito ba.

Zargin shirin kashe Yair Netanyahu

Gidan talabijin na Amurka Newsmax ya ruwaito a farkon wannan makon cewa an zargi Iran da shirya kashe Yair Netanyahu a watan Disamba na bara, lokacin da yake zaune a Florida.

Rahoton ya ce jami’an leƙen asirin Isra’ila sun sanar da hukumomin Amurka bayan sun samu labarin zargin shirin, inda Newsmax ta ruwaito hakan daga wani jami’in tsaron Amurka.

Rahoton ya fito ne bayan Benjamin Netanyahu ya shaida wa tashar Channel 14 ta Isra’ila cewa, “Iran ta kai hari kan ɗaya daga cikin ’ya’yana. Iran ta yi ƙoƙarin kashe, ta yi ƙoƙarin hallaka ɗaya daga cikin ’ya’yana.”

Newsmax ta ce an umarci Yair Netanyahu, wanda kullum yake tare da tawagar tsaron Isra’ila, da ya bar yankin nan take. An ce ya bar kayansa a wurin sannan ya dawo kai tsaye zuwa Isra’ila.

Kara karanta wannan

An shiga tashin hankali da 'yan bindiga suka hallaka shugaban APC a Kano

Rayuwar Yair a Florida

Babban ɗan Netanyahu ya shafe shekaru yana zaune a Florida, inda rahotanni suka ce “rayuwarsa mai tsada da kuma tsaron da gwamnati ke ɗaukar nauyinsa” sun sha jawo hankalin jama’a a Isra’ila.

Ci gaba da zamansa a Amurka bayan harin da Hamas ta jagoranta kan Isra’ila a ranar 7 ga Oktoba, 2023, ya jawo suka daga Isra’ilawa da dama.

Rahoton ya ce wasu Isra’ilawa sun yi tambaya kan bambancin yadda ake kallon lamarin, inda ɗan Netanyahu yake ci gaba da zama a ƙetare yayin da aka kira ɗaruruwan dubban sojojin ajiya na Isra’ila zuwa aikin soja.

Yair na sukar abokan hamayyar mahaifinsa

Yair Netanyahu, wanda ke goyon bayan ra’ayin masu tsattsauran ra’ayin dama kuma mai gabatar da shirye-shirye, yana yawan amfani da kafafen sada zumunta wajen bayyana ra’ayoyinsa kan siyasar Isra’ila.

Yana kuma yawan sukar abokan hamayyar siyasar mahaifinsa, masu sukar gwamnati da kuma ’yan jarida.

An dawo da babban yaron Netanyahu zuwa Israila
Firaministan Israila, Benjamin Netanyahu Hoto: @netanyahu
Source: Twitter

Netanyahu ya yi wa Birtaniya shagube

Kara karanta wannan

Amurka za ta janye sojojinta daga Najeriya, an sanya lokacin kwashe su

A wani labarin kuma, kun ji cewa Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu ya kira Birtaniya “Jamhuriyar Musulunci ta Birtaniya”, a wani furuci da ya yi cikin fushi.

Majiyoyi sun bayyana cewa Netanyahu ya furta haka ne ga ɗaya daga cikin​ tsofaffin ƙawayen Isra’ila a Turai.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal (Hausa Editor) Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng