Halin da Paul Biya ke Ciki da Ya Koma Kamaru bayan Kwana 73
- Shugaban ƙasar Kamaru, Paul Biya mai shekaru 93, ya dawo ƙasarsa bayan shafe kwanaki 73 a Geneva na ƙasar Switzerland
- Doguwar rashin bayyanarsa ta haifar da tambayoyi kan lafiyarsa da kuma yadda gwamnatin ƙasar ke tafiyar da harkokinta a lokacin da yake waje
- Biya, wanda ya shafe kusan rabin ƙarni yana mulkin Kamaru, ya dawo ne yayin da ake ci gaba da ce-ce-ku-ce kan makomar siyasar ƙasar
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf Kari yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru biyar, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.
Yaoundé, Kamaru – Shugaban ƙasar Kamaru, Paul Biya, ya dawo gida ranar Alhamis bayan shafe kwanaki 73 a ƙasar Switzerland, lamarin da ya sake jawo hankali kan lafiyar dattijon shugaban da kuma yadda ake tafiyar da harkokin ƙasar.
Biya mai shekaru 93 ya dawo ne birnin Yaoundé daga Geneva, inda ya kasance tun ranar 7 ga watan Yunin 2026 domin abin da fadar shugaban ƙasar ta bayyana a matsayin gajeriyar tafiya ta kashin kai.

Kara karanta wannan
Minista ya fasa kwai, an ji yadda ake shirin ƙarawa Atiku 'hawan jini' kafin zaben 2027

Source: Facebook
AP ta rahoto cewa dogon zamansa a ƙasar waje ya haifar da ce-ce-ku-ce da kuma hasashe kan lafiyarsa, musamman kasancewar ya shafe fiye da watanni biyu ba tare da bayyana a ƙasar ba.
Biya ya yi kwana 73 a waje
Rahoton ya ce jirgin da ya ɗauko shugaba Biya ya sauka a birnin Yaoundé da misalin ƙarfe 4:00 na yamma ranar Alhamis.
Biya ya bar filin jirgin sama tare da uwargidansa, Chantal Biya, inda aka gan shi yana daga hannu ga jama'a daga cikin mota yayin da suke kan hanyarsu zuwa fadar shugaban ƙasa.
Wasu magoya bayan jam'iyyar mai mulki sun taru a filin jirgin saman domin tarbar shugaban, yayin da wasu daga cikinsu ke sanye da kaya masu ɗauke da hotonsa.
Biya, wanda ya karɓi mulkin Kamaru tun a shekarar 1982, shi ne shugaban ƙasa mafi tsufa da ke kan karagar mulki a duniya a yanzu.

Kara karanta wannan
2027: ADC ta fito da bayani, an ji dalilin Atiku na ƙin sa hannu a yarjejeniyar zaman lafiya
Rashin ganin Biya ya jawo tambayoyi
France 24 ta wallafa cewa lafiyar shugaban Kamarun ta dade tana zama batun jita-jita, musamman saboda yawan tafiye-tafiyensa zuwa Geneva na ƙasar Switzerland.
A ranar 18 ga watan Yunin 2026, Ministan Sadarwa na Kamaru, René Emmanuel Sadi, ya musanta rahotannin da ke cewa an kwantar da Biya a wani asibiti da ke Geneva.
Sai dai rashin bayyanarsa ya jawo suka daga bangaren 'yan adawa, waɗanda suka ce ƙasar ta shiga wani yanayi na gibin shugabanci.

Source: Getty Images
Wasu daga cikin masu adawa sun nuna damuwa cewa ƙasar tana tafiya kamar ba ta da cikakken jagoranci, musamman yayin da ake jiran kafa sabuwar gwamnati da kuma wasu muhimman nade-nade.
Bashin Amurka ya karu
A wani labarin kuma, mun ruwaito cewa bashin ƙasar Amurka ya kai kusan dala tiriliyan 40, lamarin da ya sake haifar da muhawara kan yadda gwamnatin ƙasar ke tafiyar da harkokin kuɗinta.
Bayanai daga Ma'aikatar Baitulmalin Amurka sun nuna cewa sama da dala tiriliyan 11.5 na bashin ƙasar ya karu ne a lokacin wa'adin mulkin Donald Trump guda biyu.
Ƙarin kashe-kashen gwamnati, kuɗin ruwa kan basussuka na daga cikin abubuwan da suka ƙara nauyin bashin, yayin da 'yan siyasa ke ci gaba da cacar baki kan wanda ke da alhakin lamarin.
Asali: Legit.ng