Ana Maganar Rashin Lafiya bayan Kwana 48 Paul Biya bai Koma Kamaru ba

Ana Maganar Rashin Lafiya bayan Kwana 48 Paul Biya bai Koma Kamaru ba

  • Rashin kasancewar shugaban kasar Kamaru, Paul Biya, a gida har na tsawon kwanaki 48 ya jawo mahawara kan rashin tasirin ayyukan gwamnatin kasar
  • Jam'iyyun adawa na korafin cewa an samu babban gurbin shugabanci a kasar sakamakon jinkirin dawowar shugaban mai shekaru 93 daga Switzerland
  • Sai dai makusanta da jami'an gwamnatin kasar sun musanta zargin, inda suka jaddada cewa shugaban yana gudanar da ayyukansa kamar yadda ya kamata

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum.

Cameroon – Rashin ganin shugaban kasar Kamaru, Paul Biya, wanda yake kasar Switzerland tun farkon watan Yunin 2026, ya sake rura wutar mahawara kan jinkirin ayyukan gwamnati a kasar da al'umma ke da bukatar sauyi.

A yau Asabar an cika kwanaki 48 rabon da Biya, mai shekaru 93, wanda ya shafe sama da shekaru 40 a kan karagarsa kuma shi ne shugaban kasa mafi tsufa a duniya, da ya bar kasar Kamaru.

Kara karanta wannan

Matar aure ta kwarawa kishiyarta mai ciki ruwan zafi, ta haihu dan ya mutu

Paul Biya wajen wani taro
Shugaban kasar Kamaru, Paul Biya. Hoto: Getty Images
Source: Facebook

RFI ta rahoto cewa wata sanarwa a hukumance ta bayyana cewa ya bar kasar ne tun ranar 7 ga watan Yunin 2026 domin gudanar da "gajeren hutu a Turai" tare da matarsa Chantal Biya.

Martanin gwamnatin Kamaru

Shugaban, wanda ya sha gudanar da tsalle-tsalle akai-akai zuwa Geneva a tsawon shekarun da suka gabata, ya fuskanci jita-jita da rade-radi mabambanta game da lafiyarsa, wadanda a wani lokacin gwamnati ke musantawa.

Sakamakon rahotannin da aka wallafa a jaridu, Ministan Watsa Labarai Rene Emmanuel Sadi ya fitar da sanarwa a ranar 18 ga watan Yuni, inda ya musanta cewa ana jinyar Biya a wani asibiti da ke Geneva.

Sannan mataimakin shugaban jam’iyyar MRC, Mamadou Mota, ya bayyana a shafinsa na Facebook a ranar Juma’a cewa rashin ganin Biya yana nuna "babban gurbin shugabanci a cibiyoyin gwamnati".

Korafin 'yan kasar Kamaru

A gefe guda, Reuters ta wallafa cewa jam’iyyar adawa ta SDF a ranar Juma’a ta ce kasar tana tafiya ne kamar motar da babu direba.

Kara karanta wannan

Shugaban kasar Bangladesh ya yi murabus kafin karewar wa'adinsa

Haka zalika, masanin kimiyyar siyasa Stephane Akoa ya bayyana cewa:

"Ana ci gaba da samun rahotannin da ke nuna rikicin cikin gida tsakanin bangarori daban-daban tsakanin makusantansa."

Akoa ya kara da cewa daya daga cikin bangarorin da ke taka rawa sosai shi ne bangaren uwargidan shugaban kasa, Chantal Biya.

Ya bayyana ta a matsayin wacce ke kara kasancewa sosai a cikin huldar gwamnati tare da ambaton sunanta akai-akai wajen yanke shawarwari da gudanar da nade-nade.

Shugaban kasar Kamaru
Shugaba Paul Biya a wajen taro. Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Tinubu zai je Saudiyya

A wani labarin daban, mun ruwaito cewa Shugaba Bola Tinubu, a ranar Juma'a, ya karbi gayyata daga Yariman mai jiran gado Mohammed bin Salman bin Abdulaziz.

Jakadan Saudi Arabia a Najeriya, Yousef Albalawi ne ya mika gayyatar a ranar Juma'a yayin wata ziyara da ya kai wa Shugaban a fadar shugaban kasa da ke Abuja.

Sakon ya bayyana cewa Albalawi ya mika gayyatar ne a madadin yariman mai jiran gado na Saudi Arabiya, inda ya gayyaci Shugaba Tinubu domin halartar taron masu zuba jari a kasar.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ibrahim Yusuf avatar

Ibrahim Yusuf (Hausa Editor) Ibrahim Yusuf yana da gogewar aikin jarida da rubuce-rubucen adabi sama da shekaru hudu, kuma kwararre ne a kawo rahotannin kasuwanci, siyasa da lamuran yau da kullum. ibrahim.yusuf@corp.legit.ng