Siyasar Amurka
Shugaban Amurka, Donald Trump ya ce Kim Jong Un na Koriya ta Arewa ya amsa buƙatarsa ta tattaunawa, yayin da Amurka ke rage atisayen soji da Koriya ta Kudu.
An saki Ba’amurke mai wa’azi Kevin Rideout bayan watanni tara a hannun masu garkuwa da mutane a Nijar, inda ya sake haduwa da matarsa kafin komawa Amurka.
Tsohuwar ‘yar majalisar Amurka Marjorie Taylor Greene ta ce ana tattaunawa kan yiwuwar amfani da makaman nukiliya a yakin da ake yi da kasar Iran.
Kasar Iran ta yi watsi da barazanar Donald Trump na ayyana Mashigar Hormuz mallakar Amurka, tana mai cewa ba za a kwace ta da tweet ko ƙarfin soji ba.
An naɗa Musulma Assma Ali a matsayin alƙalin wani ƙaramin gari a Mississippi, lamarin da ya jawo mata hare-hare daga wasu ‘yan siyasa da masu amfani da sada zumunta.
Rahotanni sun ce dakarun sojojin Amurka a USS Abraham Lincoln sun fuskanci gajiya, ƙarancin abinci da matsalolin lafiya bayan shafe kwanaki 250 a teku.
Ministan Amurka, Scott Bessent ya ce Amurka za ta ɗauki tsauraran matakai kan Iran, ciki har da killace tattalin arzikinta da ci gaba da katange mashigar Hormuz.
Amurka ta soki Israel Katz bayan ya ce sojojin Isra’ila za su ci gaba da kasancewa a kudancin Lebanon, tana mai cewa hakan ya saɓa wa yarjejeniyar zaman lafiya.
Kakakin Fadar White House Karoline Leavitt za ta bar mukaminta a ƙarshen watan Agustan shekarar 2026 domin ta mayar da hankali kan yaranta da iyalinta.
Siyasar Amurka
Samu kari