Fada Zai Dawo: Trump Ya Yi Gargadi Mai Tsauri kan Iran duk da Maganar Sulhu

Fada Zai Dawo: Trump Ya Yi Gargadi Mai Tsauri kan Iran duk da Maganar Sulhu

  • Yayin da ake maganar sulhu tsakanin Amurka da Iran, Shugaba Donald Trump ya gargadi Iran cewa kasar za ta iya sake ɗaukar matakin soja
  • Trump ya ce sojojin Amurka sun kai hare-hare kan wuraren ajiyar makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuƙa, tare da cibiyoyin radar da ke bakin teku
  • Ya yi barazanar cewa idan Iran ta ci gaba da hare-harenta, Amurka za ta dauki mataki, yana mai cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba za ta ci gaba da wanzuwa ba

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.

Washington DC, US - Shugaba Donald Trump ya sake yin gargadi ga Jamhuriyar Musulunci ta Iran a yakin da ake yi.

Trump ya yi gargadin cewa har yanzu Amurka na iya ƙara ɗaukar matakin soja kan Iran bayan sababbin hare-haren da sojojinta suka kai kan wasu wuraren Iran.

Kara karanta wannan

Trump ya jawo sabon fada da Iran ta kai hare haren kan Amurka

Trump ya yi barazana ga Iran
Shugaba Donald Trump na Amurka da Mojtaba Khamenei. Hoto: @HQNewsNow, @Osocom123.
Source: Twitter

Hakan na cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, a yau Lahadi 28 ga watan Yunin shekarar 2026 da muke ciki.

Yarjejeniyar da aka cimma tsakanin Amurka da Iran

Wannan na zuwa bayan cimma yarjejeniya domin tsagaita wuta a yakin da ake yi wanda ya shafe fiye da watanni uku a yankin Gabas ta Tsakiya.

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi, ya tabbatar da cewa dakarun ƙasar za su dakatar da duk wani harin kare-kai kan Amurka da Isra'ila.

Majalisar ƙolin tsaron ƙasa ta Iran ta bayyana yarjejeniyar a matsayin "nasara ga al'ummar Iran" tare da gargaɗin Amurka kan sake yin wani kuskuren.

Iran ta yi iƙirarin cewa Amurka ta amince da haƙƙinta na tace sinadarin nukiliya a matsayin wani ɓangare na tattaunawar tsagaita wuta da za a yi.

Trump ya yi gargadi ga Jamhuriyar Musulunci ta Iran
Sabon jagoran addini a Iran, Mojtaba Khamenei. Hoto: Anadolu Ajansi.
Source: Getty Images

Barazanar da Trump ya yi kan kasar Iran

Trump ya ce sojojin Amurka sun kai hare-hare kan wuraren ajiyar makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuƙa, tare da cibiyoyin radar da ke bakin teku.

Kara karanta wannan

'Mun gama da su': Trump a fadi yadda ya kawo karshen kisan Kiristoci a Najeriya

Ya ce hare-haren sun biyo bayan abin da ya bayyana a matsayin wani sabon karya yarjejeniyar tsagaita wuta daga Iran, yana mai zargin Tehran da ci gaba da ɗaukar matakan tada rikici.

Trump ya yi gargaɗin cewa idan Iran ta ci gaba da irin waɗannan matakai, Amurka "za ta tilasta ta kammala aikin ta hanyar soja," sannan ya ƙara da cewa:

"Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba za ta ƙara wanzuwa ba."

Iran ta kai harin ramuwar gayya kan Amurka

Mun ba ku labarin cewa Iran ta kai hare-haren ramakon gayya kan wuraren da ke da alaƙa da sojojin Amurka bayan hare-haren saman da Amurka ta kai Tehran.

Iran ta kuma ƙaddamar da hare-hare da jiragen yaki zuwa kasar Bahrain bayan ta farmaki wani jirgin dakon da ya so wucewa ta mashigar Horrmuz.

Yayin da rikici ke son dawowa Gabas ta Tsakiya, gwamnatin Bahrain ta sanar da cewa harin babbar barazana ne ga tsaron ƙasar da mazauna cikinta.

Asali: Legit.ng

Authors:
Abdullahi Abubakar avatar

Abdullahi Abubakar (Hausa editor) Marubuci kuma kwararren ɗan jaridan da ya shafe shekaru 5 yana rubutu a fannin siyasa da harkokin yau da kullum. Ya kammala digirin farko a jami'ar Maiduguri. Ya samu horon aikin jarida a Reuters da AFP, ya sha halartar tarukan karawa juna sani game da bincike da adabi. Tuntube shi a abdullahi.abubakar@corp.legit.ng.