Fada Zai Dawo: Trump Ya Yi Gargadi Mai Tsauri kan Iran duk da Maganar Sulhu
- Shugaba Donald Trump ya gargadi Iran cewa Amurka za ta iya sake ɗaukar matakin soja idan Tehran ta ci gaba da abin da ya kira karya yarjejeniyar tsagaita wuta
- Trump ya ce sojojin Amurka sun kai hare-hare kan wuraren ajiyar makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuƙa, tare da cibiyoyin radar da ke bakin teku
- Ya yi barazanar cewa idan Iran ta ci gaba da hare-harenta, Amurka za ta kammala aikin soja, yana mai cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba za ta ci gaba da wanzuwa ba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Washington DC, US - Shugaba Donald Trump ya sake yin gargadi ga Jamhuriyar Musulunci ta Iran.
Trump ya yi gargadin cewa har yanzu Amurka na iya ƙara ɗaukar matakin soja kan Iran bayan sabbin hare-haren da sojojinta suka kai kan wasu wuraren Iran.
Hakan na cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na Truth Social, a yau Lahadi 28 ga watan Yunin 2026.
Trump ya ce sojojin Amurka sun kai hare-hare kan wuraren ajiyar makamai masu linzami da jiragen sama marasa matuƙa, tare da cibiyoyin radar da ke bakin teku.
Ya ce hare-haren sun biyo bayan abin da ya bayyana a matsayin wani sabon karya yarjejeniyar tsagaita wuta daga Iran, yana mai zargin Tehran da ci gaba da ɗaukar matakan tada rikici.
Trump ya yi gargaɗin cewa idan Iran ta ci gaba da irin waɗannan matakai, Amurka "za ta tilasta ta kammala aikin ta hanyar soja," sannan ya ƙara da cewa:
"Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba za ta ƙara wanzuwa ba."
Karin bayani na tafe....
Asali: Legit.ng
