Kaduna da Wasu Jihohi 12 da Za a Yi Mamakon Ruwa da Ambaliya daga Yau zuwa Kwanaki 7

Kaduna da Wasu Jihohi 12 da Za a Yi Mamakon Ruwa da Ambaliya daga Yau zuwa Kwanaki 7

  • Hukumar NiMet ta yi gargadin yiwuwar ambaliyar bazata a jihohi 13 tsakanin 11 zuwa 20 ga watan Agusta, 2026
  • Jihohin da ke cikin hadarin sun hada da Sokoto, Zamfara, Kebbi, Kaduna, Kano da wasu jihohi da dama a fadin Najeriya
  • Hukumar ta bukaci jama’a da hukumomin agaji su dauki matakan kariya tun da wuri domin kaucewa illar ambaliya

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum

Abuja, Nigeria - Hukumar Kula da Yanayi ta Najeriya (NiMet) ta yi gargadin yiwuwar samun ambaliyar ruwa ba tare da tsammani ba a jihohi 13 tsakanin ranakun 11 zuwa 20 ga Agusta, 2026.

Hukumar ta bayyana cewa gargadin na da nufin taimakawa jama’a da hukumomin da abin ya shafa wajen shirye-shiryen tunkarar ambaliyar ruwa, daukar matakan gaggawa da rage illolin bala’i.

Hukumar NiMet.
Hedkwatar hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMet) da ke Abuja Hoto: @Nimetetnigeria
Source: Twitter

NiMet ta yi gargadin ne cikin wata sanarwar yanayi da ta wallafa a shafinta na X ranar Talata, 11 ga watan Agusta, 2027.

Kara karanta wannan

Shugaba Bola Tinubu ya tabo maganar raba Najeriya saboda sabani

Jerin jihohin da NiMet ta yiwa gargadi

Hukumar ta ce jihohin da abin ya fi shafa sun hada da Sokoto, Zamfara, Kebbi, Niger, Kaduna, Nasarawa, Adamawa, Plateau, Benue, Kogi, Taraba, Cross River da Akwa Ibom.

NiMet ta ce hasashen ya yi la’akari da karfin ruwan sama da ake sa ran samu, danshin kasa, yanayin magudanan ruwa, tsarin kasa da kuma halayen madatsun ruwa.

Ambaliya na iya shafar al’umma

NiMet ta ce ambaliyar bazata na iya faruwa musamman a wuraren da ambaliyar ruwa ta saba faruwa, yankunan da suke kasa, birane da kuma al’ummomin da ke kusa da koguna.

Ta gargadi jama’a cewa ambaliyar na iya haifar da rufe hanyoyi, cunkoson ababen hawa da kuma kawo tsaiko ga harkokin sufuri.

Hukumar ta kuma ce ambaliyar na iya haifar da katsewar wutar lantarki da layukan sadarwa na wani lokaci.

Bugu da kari, ruwan sama mai karfi na iya rage gani, lamarin da zai iya kawo matsala ga zirga-zirgar ababen hawa da kuma harkokin sufurin jiragen sama.

Kara karanta wannan

Magana ta girma: An bukaci hukumomin tsaro su cafke Sheikh Jingir

An bukaci jama’a su yi hattara

Saboda haka, ta bukaci jama’a su rika bibiyar hasashen yanayi da gargadin ambaliya da NiMet da hukumomin kula da bala’o’i ke bayarwa.

NiMet ta shawarci jama’a da su guji tafiya da kafa ko tukin mota a kan hanyoyin da ruwa ya mamaye, gadoji da wuraren da ruwa ke gudana da karfi.

Ambaliya.
Yadda ruwa ya mamaye gidajen mutane sakamakon ambaliya Hoto: Getty Images
Source: Getty Images

Ta kuma bukaci mutanen da ke zaune a wuraren da ambaliya ke iya shafa da su kasance cikin shiri, tare da yin tanadin komawa wuraren da suka fi aminci idan bukatar hakan ta taso.

Ambaliya ta yi barna a jihar Neja

A wani labarin, kun ji cewa ambaliyar ruwa ta lalata kadarori da dama da darajarsu ta kaiNmiliyoyin Naira a wani sashe na rukunin gidajen Janar M.I. Wushishi da ke Minna, babban birnin Jihar Neja.

Lamarin ya sa wasu mazauna yankin suka fice daga gidajensu domin tsira da rayukansu yayin da ruwa ya mamaye gidaje da dama.

Waɗanda lamarin ya shafa sun yi kira ga gwamnatin jihar da ta gaggauta shiga tsakani tare da magance matsalar ambaliyar da kumaNabubuwan da ke haddasa ta a yankin.

Asali: Legit.ng

Authors:
Ahmad Yusuf avatar

Ahmad Yusuf (Hausa editor) Ahmad Yusuf ma'aikacin jaridar Legit.ng sashin Hausa ya fara aiki a 2021, ya kware wajen kawo labarai da rahotanni da suka shafi siyasa da al'amuran yau da kullum. Matashin ɗan jaridar ya koyi Lissafi a digirinsa na farko a Jami'ar Kimiyya da Fasaha da ke Wudil, Kano (KUST) ya kuma samu shaidar kwarewa a fannin aikin jaridar zamani daga Reuters a 2022. Kafin fara aiki da Legit Ahmad ya yi aiki da jaridu da dama na turanci da Hausa tun 2012. Mail: ahmad.yusuf@corp.legit.ng 07032379262