Hajji 2026: Za a Fassara Huɗubar Arfa zuwa Hausa da Wasu Harsuna 34 na Duniya

Hajji 2026: Za a Fassara Huɗubar Arfa zuwa Hausa da Wasu Harsuna 34 na Duniya

  • Mahukuntan Saudiyya sun sanar da cewa za a fassara hudubar Arfa ta bana zuwa harsuna 35 ciki har da Hausa da Yarbanci
  • An ce za a yada hudubar ta kafafen kafofin sadarwa na zamani domin miliyoyin alhazai da Musulmai su saurara da yarensu
  • Saudiyya ta kuma gargadi ƙasashen da ke halartar aikin Hajji su bi dokoki domin tabbatar da tsaro da nasarar aikin bana

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da biyar a aikin jarida.

Saudiyya - Mahukuntan Saudiyya sun sanar da cewa za a fassara hudubar Arfa ta bana zuwa harsuna 35 tare da yaɗa ta ta kafafen sadarwa na zamani da wasu tashoshi masu alaƙa da aikin Hajji.

An bayyana cewa matakin zai bai wa miliyoyin alhazai da Musulmai a duniya damar sauraron hudubar cikin yarensu na asali.

Saudiyya za ta fassara hudubar Arfa da Hausa da wasu harsuna 34.
Miliyoyin Musulmi a masallacin Ka'abah yayin da suke sauke faralin Hajjin 2026. Hoto: Zain JAAFAR / AFP via Getty Images
Source: Getty Images

Shugabancin harkokin addini na Masallacin Harami da Masallacin Annabi ne ya bayyana hakan, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito.

Kara karanta wannan

Hukunce hukuncen dabbobin da ya kamata a yanka domin layya

Hausa na cikin harsunan da aka zaɓa

Rahotanni sun nuna cewa harsunan da za a yi amfani da su sun haɗa da manyan harsunan duniya daga Afirka, Asiya da Turai.

Cikin harsunan akwai Turanci, Faransanci, Hausa, Yarbanci, Urdu, Indunusiyanci, Turkish, Persian, Sinanci, Rashanci, Hindi da Swahili.

Sauran harsunan sun haɗa da Somali, Punjabi, Tamil, German, Portuguese, Malay, Bosnian da Lithuanian.

Abdulrahman Sudais ya bayyana manufar fassara hudubar

Shugaban harkokin addini na Saudiyya, Sheikh Abdulrahman Al-Sudais, ya ce an shirya yin fassarar ne domin isar da saƙonnin ubangiji da koyarwar Musulunci ga Musulmai da ba sa jin Larabci.

Ya ce:

“Aikin fassarar hudubar Arfa na daga cikin manyan shirye-shiryen da aka gina bisa shekaru na gogewa domin Musulmai marasa jin Larabci su amfana da saƙonnin hudubar.”

Sudais ya ƙara da cewa an tattara manyan kayan fasaha da ƙwararrun ma’aikata domin tabbatar da hudubar ta isa ga jama’a cikin inganci.

Hudubar Arfa na daga cikin manyan hudubobin Musulunci da ake gabatarwa duk shekara a Dutsen Arafat yayin aikin Hajji.

Kara karanta wannan

Bikin Sallah: Yadda matafiya za su kauce wa cunkoso a hanyar Abuja zuwa Kaduna

Miliyoyin Musulmai a duniya kan saurari hudubar saboda muhimmancinta a addinin Musulunci.

Sheikh Abdulrahman Al-Sudais ya ce an shirya yin hudubar a yaruka daban daban don amfanar daukacin masu aikin hajji.
Dandazon Musulmai suna hawan dutsen Arfa a yayin aikin Hajjin 2026. Hoto: Ali Atmaca/Anadolu via Getty Images
Source: Getty Images

Saudiyya ta gargadi ƙasashen da ke aikin Hajji

A wani ɓangare kuma, mahukuntan Saudiyya sun sake jan kunnen ƙasashen da ke halartar aikin Hajji su bi ƙa’idojin aikin domin tabbatar da tsaro da gudanar da Hajji cikin nasara.

Sun ce ƙasashen za su ɗauki alhakin duk wata matsala da ta taso idan ba su wayar da kan alhazansu yadda ya kamata ba, kamar yadda jaridar Tribune ta ruwaito.

An kuma buƙaci shugabannin tawagogin Hajji su tabbatar alhazai suna tafiya cikin rukuni domin rage ɓacewar mutane a wuraren ibada.

Haka kuma, hukumar alhazai ta Najeriya (NAHCON) ta bayyana cewa sashen fasahar sadarwa na hukumar ya fara ƙoƙarin mayar da ayyukan Hajji gaba ɗaya zuwa tsarin fasahohin zamani.

Abin da zai faru ranar Arfar 1447

A wani labari, mun ruwaito cewa, wani abin mamaki dangane da ilimin taurari zai faru a ranar Arfa ta shekarar 2026, inda rana za ta yi daidai a saman Ka’aba a birnin Makka.

Kara karanta wannan

Trump ya yi maganar sulhu da Iran, ya fadi makomar mashigar Hormuz

Masana sun ce wannan lamari yana faruwa ne sau ɗaya cikin shekara 139 idan ya zo daidai da ranar Arfa, kuma ana sa ran zai faru a bana.

Hukumomin hasashen yanayi na Saudi sun ce lamarin ba yana nufin za a samu matsananciyar zafi ba, tare da yin karin bayani game da halin da za a shiga.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sani Hamza avatar

Sani Hamza (Hausa Editor) Sani Hamza ma'aikaci ne da ya yake da gogewa a aikin jarida. Ba fassara labarai da wallafasu a yanar gizo kadai ba, Sani yana da kwarewa a aikin rediyo da talabijin. Ya kuma shafe shekaru 8 a masana'antar fina-finai da dab'i. Imel: sanihamzafuntua@gmail.com