Sarkin Kano Muhammad Sanusi Ii
Mai martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya nada Hajiya A’in Jafaru Fagge a matsayin Jakadiyar Sarkin Kano. Nadinta na zuwa kwana biyu bayan karbar mulki.
Tsohon Sarkin Gaya, Alhaji Aliyu Abdulkadir, daya daga cikin sarakuna 5 da gwamnatin Kano ta rusa masarautunsu ya ce sun karbi wannan hakan a matsayin kaddara.
Zanga-zanga ta barke a Gaya da Nasarawa a ranar Lahadin nan kan matakin da gwamnatin jihar ta dauka na maido da Muhammadu Sanusi II a matsayin Sarkin Kano.
Biyo bayan rikicin da ya mamaye Kano, Sheikh Dahiru Bauchi ya nuna rashin jin dadi kan matakin da gwamnatin Kano ta dauka na nada sabon sarki duk da umarnin kotu.
Masarautar Bichi ta yabawa Shugaba Bola Tinubu da kuma kokarin jami'an tsaro da bangaren shari'a wurin tabbatar da zaman lafiya a Kano yayin da ake cikin wani hali.
Wata kungiyar Arewa, 'Arewa Social Contract Initiative' ta roki Sarki Aminu Bayero (da aka tube) da ya bar jihar Kano yanzu domin a samu zaman lafiya a jihar.
Rahotannin da muke samu yanzu daga jihar Kano na nuni da cewa zanga-zanga ta barke a karamar hukumar Gaya domin nuna adawa ga gwamnati kan rusa masarautu.
Kungiyar matasan Arewa ta aika da wasika ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu kan rikicin sarautar da ke faruwa a jihar Kano. Ta bukaci ya yi taka tsan-tsan.
Kungiyar 'yan kasuwan Kano sun shawarci Gwamna Abba Kabir Yusuf da ya mutunta umarnin babbar kotun tarayya wanda ya hana shi nada sabon Sarkin Kano.
Sarkin Kano Muhammad Sanusi Ii
Samu kari