Sarkin Kano: Matasan Arewa Sun Rubuta Wasika Ga Tinubu, Sun Yi Muhimmin Gargadi

Sarkin Kano: Matasan Arewa Sun Rubuta Wasika Ga Tinubu, Sun Yi Muhimmin Gargadi

  • Ƙungiyar matasan Arewa ta akka da wasiƙa ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan rikicin sarautar Kano
  • Ƙungiyar ta buƙaci shugaban ƙasan da ya yi taka tsan-tsan da wasu da ke cikin gwamnatinsa masu son kawo rikici a jihar Kano
  • Ta yi gargaɗin cewa yunƙurin dawo da Aminu Ado Bayero kan sarauatar Kano ba komai ba ne illa ƙoƙarin yi wa tanadin doka karan tsaye

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Kano - Ƙungiyar majalisar matasan Arewa ta rubuta wasiƙa ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu kan rikicin sarautar Kano.

Ƙungiyar ta shawarci Shugaba Tinubu da ya yi taka tsan-tsan da wasu da ke cikin gwamnatinsa da ke shirin haifar da rikici a jihar Kano.

Kara karanta wannan

Sarkin Kano: 'Yan kasuwa sun ba Gwamna Abba shawara kan abin da ya kamata ya yi

An ba Tinubu shawara kan rikicin sarautar Kano
Majalisar matasan Arewa ta bukaci Tinubu ya yi taka tsan-tsan kan rikicin sarautar Kano Hoto: Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, Sanusi Lamido Sanusi, Alhaji Aminu Ado Bayero
Asali: Facebook

Jaridar The Punch ta ce wasiƙar mai ɗauke da kwanan watan 25 ga watan Mayun 2024, tana ɗauke da sa hannun shugaban ƙungiyar Dakta Ali Idris da sakatarenta, Dakta Garba Abdulhafiz.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Wasiƙar kuma an tura kwafinta zuwa ga ofishin majalisar ɗinkin duniya, ƙungiyar tarayyar Turai, ƙungiyar ECOWAS da sauransu, rahoton jaridar Leadeship ya tabbatar.

Wane gargaɗi aka yi wa Tinubu?

Wasiƙar ta yi nuni da cewa sauyin da aka samu a dokar masarautun jihar ya samu ne sakamakon dokar da majalisar dokokin jihar ta amince da ita, sannan duk wani ƙoƙarin sauya dokar zai haifar da rikici.

Ƙungiyar ta bayyana cewa yunƙurin dawo da Aminu Ado Bayero kan sarauta ba komai ba ne face ƙoƙarin yi wa doka karan tsaye.

Wani ɓangare na wasiƙar na cewa:

"Wannan mummunan lamarin abin kunya ne ga gwamnatinka da ƙimarka a matsayin wanda a koda yaushe yake bayyana kansa a matsayin ɗan dimokuraɗiyya."

Kara karanta wannan

Sanusi II vs Aminu Ado: Atiku ya yi magana kan rikicin sarautar Kano, ya fadi mai laifi

"Tsoronmu shi ne gwamnatinka da waɗanda ka ba muƙamai, za a iya yi musu kallon mutanen da ba su mutunta mulkin dimokuraɗiyya da kundin tsarin mulki."
"Muna son mu jawo hankalinka a wannan gaɓar cewa Kano ta kasance cikin zaman lafiya."
"Sannan duk wani ƙoƙarin kawo hargitsi a jihar ta hanyar biyewa wasu tsiraru masu son kansu saɓanin abin da mutane miliyan 20 suke so, zai haifar da ruɗani da rikici kuma zai ɓata sunsn gwamnatinka."

Rawar da Tinubu ya taka a naɗin Sarkin Kano

A wani labarin kuma, kun ji cewa Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya bayyana rawar da shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya takaa wajen dawo da shi kan sarauta.

Sarkin na Kano ya bayyana cewa shugaban ƙasan bai yi katsalandan ba wajen dawo da shi kan sarauta duk kuwa da matsin lambar da aka yi masa kan ya yi hakan.

Asali: Legit.ng

Authors:
Sharif Lawal avatar

Sharif Lawal Sharif Lawal ma'aikacin jarida ne wanda ya samu gogewa a harkar aikin jarida. Ya yi digirinsa na farko a jami'ar Ahmadu Bello (ABU) da ke Zaria. Ya samu horo daga Reuters kan aikin jarida da tantance labarai. Za a iya tuntubarsa ta Sharif.lawal@corp.legit.ng