Jihar Rivers
Majalisar wakilan Najeriya ta bayyana cewa ta na da masaniya a kan matakin da shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya dauka na dakatar da gwamnatin Ribas.
Jam'iyyar APC ta gargadi gwamnan jihar Osun bayan Bola Tinubu ya dakatar da gwamnan Rivers, Fubara. APC ta ce ko gwamnan Osun ya bi doka ko a dakatar da shi.
Gwamnan jihar Rivers, Siminalayi Fubara ya yi bayani na farko bayan Bola Tinubu ya dakatar da shi daga gwamna. Tinubu ya dakatar da Fubara da 'yan majalisar Rivers.
Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Alhaji Atiku Abubakar ya soki matakin da shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya ɗauka dangane da rikicin siyasar jihar Ribas.
PDP ta ce yi watsi da dokar ta baci da Tinubu ya ayyana a Rivers da dakatar da Gwamna Fubara, tana mai cewa, hakan ya saba wa doka. Ta nemi a mutunta dimokuradiyya.
Sojoji da manyan motocin yaki sun mamaye gidan gwamnatin Rivers bayan dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara da mambobin majalisar jihar har na watanni shida.
Shugaba Tinubu ya yi amfani da sashe na 305(1)–(6) na kundin tsarin mulki na 1999 da ya ba wa shugaban ƙasa damar ayyana dokar ta ɓaci wajen dakatar da Fubara.
Shugaban ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya naɗa gwamnatin rikon kwarya a jihar Ribas jim kaɗan bayan sanar da dakatar da Gwamna Fubara da mataimakiyarsa.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya shiga tsakani kan rikicin siyasar da ke aukuwa a jihar Rivers. Ya dakatar da Gwamna Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa.
Jihar Rivers
Samu kari