Gasar kwallo
Hukumar kwallon kafa ta duniya FIFA ta fitar da jadawalin ne a yau Alhamis 15 ga watan Faburairu wanda ya kunshi kasashen Afirka da sauran kasashen duniya.
Dan wasan tawagar Super Eagles, Sadiq Umar ya yi martani kan caccakar Alex Iwobi da ake yi a kafafen sadarwa inda ya ce shi ba Iwobi ba ne a yi hankali.
Shugaban kasa Bola Tinubu ya baiwa daukacin ‘yan kungiyar Super Eagles lambar karramawa ta kasa ta 'Member of the Order of Niger (MON), da kyautar gidaje a Abuja.
Shugaban kasa Bola Tinubu ya jinjinawa kungiyar Super Eagles ta Najeriya bisa jajircewar da suka nuna a wasan karshe na gasar cin kofin nahiyar Afirka (AFCON)
A ranar Lahadi, 11 ga watan Fabrairu ya kamata a daura auren mataimakin Bursar na jami'ar jihar Kwara, Ayuba Olaitan, wanda ya rasu yayin kallon wasan Najeriya.
Wani ‘dan Najeriya wanda ya yi hasashen sakamakon AFCON a matakin rukuni, ya yi hasashen cewa Najeriya za ta yi nasara kan Ivory Coast a wasan karshe.
Fasto Dakta Kan Ebube Muonso ya yi hasashen kasar da za ta lashe gasar AFCON a gobe Lahadi 11 ga watan Faburairu inda ya ce Ivory Coast ce da nasara.
Wani ‘dan Najeriya ya ce zai fi kyautuwa mutum ya guji kallon wasan Najeriya da Ivory Coast idan har ya san yana da hawan jini. Ya ce zai fi kyau a bi sakamakon.
A yayin karo tsakanin Najeriya da Afrika ta Kudu a wasan kusa da karshe na gasar cin kofin Afrika, AFCON, akalla ‘yan Najeriya biyar ne suka mutu saboda zullumi.
Gasar kwallo
Samu kari