Jerin Kasashen Nahiyar Afrika 10 da Suka Fi Kowa a Jadawalin Hukumar FIFA Bayan Kallama Gasar AFCON

Jerin Kasashen Nahiyar Afrika 10 da Suka Fi Kowa a Jadawalin Hukumar FIFA Bayan Kallama Gasar AFCON

Kawanaki kadan bayan kammala gasar AFCON a kasar Ivory Coast, Hukumar FIFA ta cire jadawalin kasashe kamar yadda ta saba.

Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

Hukumar FIFA ta fitar da jadawalin ne a yau Alhamis 15 ga watan Faburairu wanda ya kunshi kasaseh da dama a duniya.

FIFA ta fitar da jadawalin kasashen Afirka da suka fi kokari
Jerin Kasashen Afrika 10 da a Jadawalin Hukumar FIFA. Hoto: @ng_supereagles, @BafanaBafana.
Asali: Twitter

Jerin kasashen Afirka a jadawalin

Kamar yadda jadawalin ya ke, Najeriya ta kasance na uku yayin da kasar Ivory Coast da ta lashe gasar AFCON ta ke mataki na biyar.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Legit Hausa ta jero muku jadawalin kasashen Afirka guda 10:

1. Morocco

Morocco ita ce ta farko a Nahiyar Afirka yayin da ta ke mataki na 12 a duniya baki daya bayan ta samu karin mataki daya.

Kara karanta wannan

Hukumar Hisbah ta aikawa ‘yan iskan gari sako da aka daure Murja Kunya a kurkuku

2. Senegal

Kasar Senegal da Ivory Coast ta cire a gasar AFCON ta tsallako zuwa mataki na biyu yayin da ta ke mataki na 17 a duniya.

3. Najeriya

Bayan rasa nasara a wasan karshe a gasar AFCON, Najeriya ta samu nasarar kasancewa ta uku yayin da ta tsallako daga mataki na 42 zuwa 28 a duniya.

4. Masar

Masar ta yi rashin nasara inda ta sauko kasa inda yanzu ta ke mataki na hudu a Afirka yayin da ta ke mataki na 36 a duniya.

5. Ivory Coast

Duk da nasarar lashe gasar AFCON, Ivory Coast ta hauro mataki na biyar daga na 10 a Afirka yayin da ta ke mataki na 39 a duniya.

6. Tunisia

Kasar Tunisia ta kasance na shida a Nahiyar Afirka yayin da haura daga mataki na 54 zuwa na 41 a duniya.

7. Algeria

Algeria ita ce kasa da ke mataki na bakwai a Afirka yayin da samu koma baya a duniya inda ta ke mataki na 43.

Kara karanta wannan

AFCON: Mourinho ya fadi kasar da ya ke so ta lashe gasar, ya tura sako ga abokinsa, Peseiro

8. Mali

Mali ita ce kasar ta takwas a Nahiyar Afirka yayin da ta samu karin girma a duniya inda ta ke mataki na 47.

9. Kamaru

Kasar Kamaru da ke makwabtaka da Najeriya ta na mataki na tara a Afirka yayin da samu karuwa a duniya a mataki na 51.

10. Afirka ta Kudu

Kasar da Najeriya ta yi waje da ita a gasar AFCON ita ce ta 10 a Afirka yayin da ta ke mataki na 58 a duniya.

Sadiq ya gargadi ‘yan Najeriya

Kun ji cewa dan wasan gaban Super Eagles, Sadiq Umar ya gargadi masu caccakarsu bayan rashin nasara a AFCON.

Umar ya ce shi ba kaman Alex Iwobi ba ne da za su saka shi a gaba wurin sukarsa bayan kammala gasar.

Asali: Legit.ng

Online view pixel