Masu Garkuwa Da Mutane
Kwamishinan yada labarai a jihar Benue, Matthew Abo ya shaki iskar 'yanci da safiyar yau Alhamis 5 ga watan Oktoba, an sace kwamishinan ne a gidansa da ke Zaki-Biam.
Jami'an 'yan sanda sun kwamushe wani da ake zargin ya na bai wa 'yan bindiga bayanan sirri da ya kai ga sace daliban Jami'ar FUDMA a jihar Katsina.
Miyagun ƴan bindiga sun kai wani sabon hari a jihar Kaduna inda suka yi awon gaba da mutane masu yawa. Ƴan bindigan sun halaka mutum ɗaya tare da sace wasu mutum 19.
Wata mahaifiya ta yi ta maza inda ta cafke wani ɗan ta'adda da ya save ɗiyarta sannan ya halaka ta bayan an ba shi kuɗin fansa masu yawa a Zariya.
Masu garkuwa da mutane da suka sace kwamishinan yaɗa labarai na jihar Benuwai sun nemi iyalinsa sun harhaɗa masa Naira miliyan N60m a matsayin fansa.
Rundunar Tsaro a Najeriya ta nemi hadin kan al'umma wurin yakar ta'addanci a kasar, rundunar ta ce ita kadai ba za ta iya kawo karshen matsalar tsaro ba.
Wani dan bindiga ya gamu da tsautsayi yayin da ya je sace makwabcinsa, Alhaji Mohammed Makasudi a jihar Neja, mai gidan ya harbe shi a kafa yayin sace shi.
Tsohuwar minista a lokacin gwamnatin Buhari, Sadiya Farouk ta shiga jerin masu gangami don ceto daliban da aka sace a Jami'ar Gwamnatin Tarayya da ke jihar Zamfara.
Gwamnan jihar Benue, Hyacinth Alia, ya yi kakkausan martani kan sace kwamishinan watsa labarai na jihar da wani tsohon shugaban ƙaramar hukumar Ukum ta jihar.
Masu Garkuwa Da Mutane
Samu kari