Wahalar man fetur a Najeriya
Shugaban kamfanin man fetur na Najeriya, Mele Kyari ya tabbatar wa ƴan ƙasar cewa nan da shekaru 10 za a daina wahalar fetur. Ya bayyana hakan a Abuja.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya bayyana cewa matakin da ya dauka domin cire tallafin man fetur, ya dauke shi ne domin tabbatar da gaskiya a bangaren makamashi.
Tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya bayyana adadin man fetur din da ake sacewa a Najeriya. Obasanjo ya ce satar ta durkusar da tattalin arzikin kasar nan.
Gwamnatin tarayya ta shirya fara bada tallafin N25,000 ga 'yan Najeriya duk wata domin rage radadin halin matsin tattalin arziki da tsadar rayuwa da ake fama da su.
Gwamnatin tarayya ta sanar da dakatar da fitar da iskar gas din dafa abinci zuwa kasashen waje domin rage karanci da tashin gwauron zabin farashinsa a kasar.
Masu sayar da fetur a bayan fage da aka fi sani da 'yan bumburutu sun fara sayar da lita 1 akan naira 1,000 yayin da aka fara wahalar mai a Legas, Abuja da Ogun.
Kungiyar masu motocin haya ta Najeriya (NARTO), ta dakatar da yajin aikin da ta shirya yi a fadin kasar biyo bayan ganawar da suka yi da gwamnatin tarayya.
Wani mutum ya nuna kaduwarsa kan farashin da ya siya man fetur a jihar Enugu. Mutumin ya nuna shaida sannan ya bayyana sunan gidan man da ya siye shi kan haka.
Matakin dakatar da ayyuka manyan tankokin dakon man fetur da ƙungiyar NARTO ta ɗauka ya haddasa dogon layi da ƙarancin kan fetur a birnin tarayya Abuja.
Wahalar man fetur a Najeriya
Samu kari