Arewa
Kusoshin PDP a Arewa ta Tsakiya za su nada shugaban riko na kasa daga yankin. Shugabanni sun yi kira ga hadin kai da bin kundin tsarin PDP don ci gaba.
Kamfanin rarraba wuta na TCN ya ce an kai hari kan layin wutar 330kV Shiroro Katampe kuma an sace wasu muhimman kayayyaki. TCN na kokarin gyara wutar da aka lalata.
Wani manomi ya rasa rayuwarsa yayin da wasu mutum huɗu suka samu raunuka da wani abu da ake zaton bom ne ya tarwatse a yankin karamar hukumar Shiroro aNeja.
Gwamna Ahmed Aliyu na jihar Sakkwato ya samu nasarar zama gwarzon shekara a fannin raya birane da gina gidaje, an ba shi lambar yabo a birnin Abuja.
Masu ruwa da tsakin PDP a shiyyar Arewa ta Tsakiya sun jaddada cewa suna nan a kan bakarsu ta samar da wanda zai maye gurbin shugaban jam'iyya, Damagum.
Gwamna Umar A. Namadi na jihar Jigawa ya fatattaki daya daga cikin hadiminsa mai suna Khadijah Sidi Sulaiman daga mukaminta a yau Laraba 18 ga watan Disambar 2024.
Kungiyar APC, Arewa ta Tsakiya ta goyi bayan Tinubu ya yi tazarce a 2027, tana jaddada amfanin mulkinsa, duk da rashin goyon bayan ACF da AYCF da wannan kuduri.
An samu yawaitar masu garkuwa da mutane a yankin Arewacin Najeriya a 2024. Hakan ya sanya gwamnonin Arewa aik da 'yan sa kai domin yakar 'yan bindiga
Solomon Arase ya ce Buhari ginshiki ne na haɗin kai, tare da gode masa kan jajircewarsa wajen tsaro, yaki da cin hanci da kuma tabbatar da cigaban Najeriya.
Arewa
Samu kari