Arewa
Shugabannin 'yan bindiga a Arewacin Najeriya sun bayyana cewa, yanzu kam sun gama aikin ta'addanci, za su ajiye makamai su rungumi zaman lafiya kowa ya huta.
Babbar kotun da ke zamanta a Ilorin da ke jihar Kwara ta yanke hukuncin kisa kan wani Mohammed Kazeem da zargin ya kashe makwabcinsa ana daf da daura aurensa.
Masu garkuwa sun afkawa fadar sarkin Gurku, Jibrin Mohammed a jihar Nasarawa tare da sace shi da mai dakinsa, jami'an 'yan sanda sun bazama cikin daji ceto su.
Gwamna Dakta Agbu Kefas na jihar Taraba ya samu sahalewar majalisar dokokin jihar na karɓo rance kuɗi daga bankuna huɗi, waɗanda suka kai Naira Biliyan N206bn.
Gwamna Nasiru Idris na jihar Kebbi ya kafa tawagar wakilai da zasu tafi jamhuriyar Benin domin ceto matasan jiharsa su 10 da aka tsare bisa kuskure a Kotano.
Rundunar 'yan sandan Kano ta kama mutane fiye da 60 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban da suka hada da dabanci da kwacen motoci da babura a birnin Kano.
Wata mata mai suna Hauwau Abubakar ta maka mahaifiyarta a kotu don ta nemo mata mahaifinta ganin yadda kannenta da suke zama wuri daya su ke mata gori a kullum.
Wani Farfesa da ke jami'ar Gwamnatin Tarayya da ke Dutsin-Ma, Bashir Aliyu Sallau a jihar Katsina ya rungumi sana'ar wanzanci duk da koyarwa da ya ke a jami'a.
Sojin sama sun yi luguden wuta kan 'yan bindiga tare da kashe manyansu biyu da suka hada da Ado Aliero da Dankarami a wani hari da suka kai a jihar Zamfara.
Arewa
Samu kari