Abun Bakin Ciki
Gwamnan jihar Bauchi, Bala Abdulkadir Mohammed ya sanar da rasuwar kawunsa kuma Sarkin Alkaleri, Alhaji Muhammadu Abdulkadir, wanda ya rasu yana da shekaru 100.
Wani jami'in ‘yan sanda da ya sha giya ya bugu ya harbe wani mutum a yankin Maitumbi, jihar Neja. Rundunar ‘yan sanda ta fara bincike tare da farautar jami’in nata.
Rahotanni sun bayyana cewa masu zanga-zanga sun ɓarnata fadar sarki da sakateriyar ƙaramar hukumar Gwer ta Yamma a jihar Benue kan kisa jami'an tsaro 3.
Tsohon ƙaramin minista a ma'aikatar kula da harkokin kasashen waje, Dubem Onyia ya kwanta dama yana da shekaru 73 a duniya, an fara jimamin rashinsa.
Shugaba Tinubu ya yi jimamin rasuwar Farfesa Chukkol, masanin shari’a daga ABU Zaria, yana mai jinjina ga gagarumar gudunmawarsa a fannin ilimi da shari’a.
‘Yan ta’addar Lakurawa sun kashe mutum 13 a Birnin Dede, Kebbi, sun kona kauyuka 7, a ramuwar gayya bayan kisan shugabansu Maigemu da dakarun tsaro suka yi.
Tsohon mataimakin gwamnan jihar Kogi, Chief Patrick Adaba, ya rasu yana da shekaru 79 a ranar Lahadi a Abuja, bayan fama da gajeriyar rashin lafiya.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya fadi rawar da marigayi Abba Kyari ya taka wurin cire Joy Nunieh daga mukamin shugabar rikon kwarya a hukumar NDDC.
Rahotanni sun tabbatar da cewa yan bindiga da ake zaton yaran Bello Turji ne sun sace wani mutum da ya bayyana kansa a bidiyo a matsayin ɗan Ishyaka Rabiu.
Abun Bakin Ciki
Samu kari