Bola Tinubu
Shugaba Bola Tinubu ya ba ministocinsa sabon umarni kan nunawa yan Najeriya abin da suka tsinana yayin da gwamnati ke cika shekara daya a kan mulki.
Shugaban Bola Tinubu ya maye gurbin yaron Nyesom Wike, Chukwuemeka Woke da Dakta Adedeji Ashiru a matsayin daraktan hukumar Ogun-Osun River Basin.
Ministan kasafi da tsare-tsare a Najeriya, Atiku Bagudu ya fito fili ya ba ƴan kasar hakuri kan halin kunci da ake ciki inda ya kare matakan da Bola Tinubu ke dauka.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da nadin sabon shugaban hukumsr kiyaye hadura ta kasa (FRSC). ACM Shehu Mohammed ya samu sabon mukamin.
Gwamnatin tarayyar Najeriya ta bayyana cewa tsauraran matakan da gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta bijiro da su ne suka ceto tattalin arzikin kasar daga durkushewa.
Tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar APC ta kasa a Arewa maso Yamma, Salihu Lukman ya nuna damuwa kan salon mulkin Bola Tinubu ganin yadda ake tafiyar da gwamnati.
Fitaccen ɗan fafutuka a soshiyal midiya wanda ake kira da VDM ya ce Bola Tinubu ya fi ƙarfin Atiku da Kwankwaso da Peter Obi ko da kuwa sun haɗa kai a 2027.
Ma'aikatar fasaha da al'adu ta tarayya ta ware N290m daga cikin kasafin kudinta domin sanya fitilu masu amfani da haske rana a mahaifar minista Hannatu Musa Musawa.
Wani jigo a jam'iyyar All Progressives Congress (APC), Ismaeel Ahmed, ya wanke shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu daga zargi kan halin da kasar nan ta tsinci kanta.
Bola Tinubu
Samu kari