Yanzun nan Rigima Ta Barke a Majalisar Wakilai kan Bukatar a Gayyaci Tinubu
- An hargitse a zaman majalisar wakilai da aka gabatar da bukatar a gayyaci Shugaba Bola Tinubu ya yi bayani kan jinkirin aiwatar da kasafin 2025
- Benedict Etanabene ya fara cewa sabon umarnin da Akanta Janar ya fitar zai iya kawo cikas ga aiwatar da ayyukan mazabu da kasafin kudin bana
- Kudurin da aka gabatar na gayyatar shugaban kasa ya haifar da cacar baki tsakanin 'yan majalisar yayin zaman da aka gudanar yau ranar Laraba
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Sani Hamza ƙwararren edita ne a fannin nishaɗi, al'amuran yau da kullum, da kuma siyasa, wanda ke da shekaru sama da biyar a aikin jarida.
Abuja - An samu rikici a zaman majalisar wakilai a ranar Laraba bayan 'yan majalisar sun samu sabani kan wani kudiri da ke neman a gayyaci Shugaba Bola Ahmed Tinubu.
An rahoto cewa kudirin da ya jawo ce-ce-ku-cen ya bukaci a gayyaci Tinubu domin ya yi bayani kan jinkirin aiwatar da kasafin kudin shekarar 2025.

Source: Twitter
Lamarin ya faru ne bayan dan majalisa mai wakiltar mazabar Okpe/Sapele/Uvwie ta jihar Delta, Benedict Etanabene, ya gabatar da batu na gaggawa, kamar yadda The Cable ta ruwaito.
Etanabene ya ja hankalin majalisar kan wata takarda da Akanta Janar na Tarayya, Shamseldeen Ogunjimi, ya fitar ranar 29 ga Yuni.
A cikin takardar, an umurci dukkan ma'aikatu, hukumomi da cibiyoyin gwamnatin tarayya da su dakatar da biyan kudaden ayyukan mazabu da na shiyyoyi (ZIPs), sai dai idan Ma'aikatar Harkokin Musamman da Hulda Tsakanin Gwamnatoci ta tantance su.
Dan majalisar ya bayyana cewa wannan mataki na iya kawo cikas ga aiwatar da kasafin kudin shekarar 2025, musamman ayyukan da aka ware wa mazabu.
Saboda haka, ya bukaci majalisar ta gayyaci Shugaba Tinubu domin ya yi wa 'yan majalisar bayani kan jinkirin aiwatar da kasafin kudin bana da kuma sabon umarnin da aka bayar.
Bukatar tasa ta haifar da cacar baki tsakanin 'yan majalisar, lamarin da ya janyo hargitsi a zauren majalisar.
Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, ba a bayyana matakin da majalisar za ta dauka kan bukatar gayyatar shugaban kasar ba.
Asali: Legit.ng
