Halin da Ake Ciki da Yan Sanda Suka Tabbatar da Hari kan Ayarin Motocin Peter Obi
- Rundunar ’yan sandan jihar Benue ta yi kan harin da aka kai kan ayarin Peter Obi yayin da yake kan hanyarsa zuwa Yelwata
- ’Yan sanda sun ce har yanzu ba a gano dalilin matasan suka tare ayarin Obi ba, yayin da aka fara bincike domin gano cikakken bayani
- Jam’iyyar NDC ta zargi APC da shirya matasan, yayin da ita kuma ta musanta zargin, tana cewa ba ta da hannu cikin lamarin
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Makurdi, Benue - Rundunar ’yan sandan Benue ta tabbatar da cewa an kai wa ayarin ɗan takarar shugaban ƙasa na NDC, Peter Obi, hari a hanyar Gboko-Makurdi.
Lamarin ya faru ne a ranar Talata, yayin da Obi yake kan hanyarsa zuwa Yelwata da ke ƙaramar hukumar Guma domin ziyartar waɗanda harin ya shafa.

Source: Facebook
Jami’in hulɗa da jama’a na rundunar, DSP Peter Orchia Aondongu, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana cewa ’yan sanda sun samar da tsaro, cewar Leadership.
Sai dai rundunar ta ce ba a san dalilin da ya sa wasu matasa suka tare ayarin Obi ba, tana mai cewa an fara bincike.
Ya ce jami’an tsaro sun raka Obi yayin tafiyarsa zuwa Yelwata, amma har yanzu ba a gano dalilin da ya sa matasan suka tare ayarin ba.
Aondongu ya ce rundunar tana sane da lamarin da ya shafi tafiyar Peter Obi zuwa Yelwata, inda jami’an ’yan sanda suka samar da tsaro.
Ya ƙara da cewa ana sa ido kan lamarin tare da gudanar da bincike domin gano dalilan da suka haifar da toshe hanyar ayarin.
Rundunar ta bayyana cewa za ta fitar da ƙarin bayani yayin da ake samun sabon ci gaba game da binciken lamarin.
A baya, an ruwaito cewa ɗimbin matasa sun tare ayarin Obi a hanyar Gboko-Makurdi, lamarin da ya hana shi ci gaba zuwa Yelwata.
Obi ya je Makurdi, babban birnin Benue, da safiyar Talata, inda yake shirin zuwa Yelwata domin jajanta wa waɗanda harin ta’addancin ya shafa.
An shirya ziyarar ne domin Obi ya gana da waɗanda lamarin ya shafa tare da nuna goyon baya ga iyalan da al’ummomin da abin ya shafa.
Sakataren yaɗa labarai na NDC a Benue, Agile Bem Ordedoo, ya zargi APC da tattara matasan domin hana Obi shiga Yelwata.
Ordedoo ya ce dubban ’yan daba ne aka tattara suka tare ɗan takarar shugaban ƙasa na NDC, Peter Obi, yayin da yake kokarin shiga Yelwata.
Ya bayyana cewa Obi ya shirya ziyartar waɗanda harin ya shafa tare da kai musu kayan agaji masu darajar biliyoyin naira.
Sai dai APC ta musanta zargin, tana mai cewa ba ta da masaniya kan lamarin kuma ba za ta shiga harkar daba ba.
Sakataren yaɗa labarai na APC a Benue, Benedict Yaweh, ya ce ba su da masaniya kan harin idan da gaske an kai masa a Makurdi.
Ya ce idan har an kai wa Obi hari, akwai yiwuwar wasu magoya bayansa da ba su ji daɗi ne suka aikata hakan, ba ’yan APC ba.
Yaweh ya ce APC jam’iyya ce mai son zaman lafiya, kuma ba ta shiga ayyukan daba ko tashin hankali.
Sabani tsakanin bangarorin ya zo ne bayan rundunar ’yan sanda ta tabbatar da cewa wasu matasa sun tare ayarin Obi.
Sai dai rundunar ta jaddada cewa har yanzu ba ta gano dalilin da ya sa matasan suka ɗauki wannan mataki ba.
’Yan sanda ba su bayyana sunayen matasan da suka tare ayarin ba, sannan ba su danganta lamarin da wata jam’iyya ko wani mutum ba.
Karin bayani na tafe....
Asali: Legit.ng


