Da Gaske an Sauya Dan Takarar Gwamna a Adamawa? ADC Ta Bayyana Gaskiya
- Jam'iyyar ADC a Adamawa ta yi martani kan rahotannin da suke yawo game da maye gurbin ɗan takararta, Ambasada Injiniya Umar Suleiman
- Jam'iyyar ta ce Umar Suleiman ne halastaccen ɗan takara, babu batun janye takara, maye gurbinsa ko wata tattaunawar sauya sunansa
- ADC ta ce shugabannin ƙananan hukumomi 21 sun tabbatar da goyon bayansu gare shi, tare da roƙon al'umma su yi watsi da jita-jita
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Yola, Adamawa - Jam'iyyar ADC reshen jihar Adamawa ta yi martani kan rahoton sauya dan takarta na gwamna da ake yadawa.
Jam'iyyar ADC ta musanta rahoton wata fitacciyar jarida da ta yi ikirarin cewa za a maye gurbin ɗan takararta na gwamna a zaɓen 2027, Injiniya Umar Suleiman.

Source: Twitter
Hakan na cikin wata sanarwa da Darakta Janar na Kwamitin Yaƙin Neman Zaɓen Injiniya Umar Suleiman, Dattijo Mark Wosi ya sanya wa hannu, cewar Tribune.
Adamawa: ADC ta ƙaryata sauya dan takarar gwamna
Jam'iyyar ta bayyana rahoton a matsayin ƙarya da masu adawa da ita suka ƙirƙira domin cimma manufar siyasa ta karan kansu.
ADC ta ce Ambasada Injiniya Umar Suleiman ne halastaccen kuma amintaccen ɗan takarar gwamna da aka zaɓa a Adamawa. Ta ce babu wani sauyi game da takararsa.
Sanarwar ta jaddada cewa babu batun maye gurbinsa, janye takara, sauka daga takara ko kuma wata tattaunawa da ake yi kan sauya ɗan takarar gwamna. Jam'iyyar ta buƙaci masu kaɗa ƙuri'a da su yi watsi da jita-jitar da aka ƙirƙira domin yaudarar jama'a.

Source: Facebook
Goyon baya da ɗan takarar gwamna ya samu
ADC ta kuma bayyana cewa goyon bayan da shugabannin ƙananan hukumomi 21 na jihar suka nuna wa Umar Suleiman ya ƙara tabbatar da haɗin kan jam'iyyar da kuma ingancin takararsa.
Jam'iyyar ta ce har yanzu ta mayar da hankali kan aiwatar da manufofinta na yaƙin neman zaɓe ƙarƙashin taken "Ingantacciyar Adamawa", tana mai kira ga magoya bayanta su ci gaba da tsayawa tsayin daka duk da abin da ta bayyana a matsayin yaɗa bayanan ƙarya.
ADC ta kuma roƙi al'ummar jihar Adamawa da su yi watsi da jita-jitar da ake yaɗawa, tare da ci gaba da bai wa ɗan takararta na gwamna goyon baya yayin da ake tunkarar zaɓen shekarar 2027.
Tsagin ADC ta dakatar da Atiku, Babachir
An baya, kun ji cewa Wani tsagi na ADC a jihar Adamawa ƙarƙashin Raji Zumo ya yi taron sanar da dakatar da Atiku Abubakar da wasu mutane biyu daga jam'iyyar.
Raji Zumo ya zargi Atiku da sauran mutanen da hannu wajen ƙirƙirar rassan bogi a jam'iyyar, raunana tsarin shugabanci, da yin watsi da umarnin kotu.
Sai dai Babachir Lawal, wanda shi ma aka dakatar da shi, ya bayyana kwamitin Raji a matsayin "masu shan wiwi" wadanda ƙwaya ta bugar.
Asali: Legit.ng

