Matar Tsohon Sanata Ta Shiga Matsala, Minista Ya Bukaci Gudanar da Bincike Kanta
- Ministan sufurin jiragen sama, Festus Keyamo, ya umarci a gudanar da bincike kan matar tsohon sanata a Najeriya
- Ana zargin matar tsohon sanata Elisa Abbo da shiga wuraren da aka haramta a filin jirgin saman Yola da ke Adamawa
- Bidiyon da aka samu ya nuna matar tana raka mijinta har zuwa matattakalar jirgi, lamarin da ya jawo maganganu
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne ta bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru biyar.
Yola, Adamawa - Ministan sufurin jiragen sama da bunkasa sararin samaniya, Festus Keyamo, ya buƙaci bincike kan matar tsohon sanata.
Keyamo ya bayar da umarnin gudanar da cikakken bincike kan matakan tsaro a filin jirgin saman Yola bayan rahotanni sun bayyana karya dokokin tsaro.

Source: Facebook
Premium Times ta ce matakin ya biyo bayan wallafa wasu bidiyoyi da suka nuna matar Sanata Ishaku Abbo tana saba ka'ida.
Yadda matar tsohon sanata ta saba ka'ida
An nuna matar tana shiga wuraren da aka kebe ga ma'aikata da fasinjoji kawai wanda hakan ya saba ka'ida a hukumar.
Rahotanni sun ce ministan ya bukaci jami'an tsaro su yi bayani kan yadda lamarin ya faru bayan rahoton farko ya bayyana, lamarin da ya jawo hankalin ma'aikatar.
Jami'an tsaron filin jirgin sun ce Patience Abbo ta sanar da su cewa tana tafiya tare da mijinta, saboda haka aka ba ta damar wucewa ta kofar shiga.
A cewar shugaban tsaro na filin jirgin, jami'an sun fahimci cewa ba fasinja ba ce kawai bayan sun ga ta dawo ita kadai daga yankin da jirgin yake.
Sai dai wani sabon bidiyo da aka samu daga baya ya nuna ta sake rakiyar mijinta zuwa kusa da matakalar jirgi tana tura wata akwati mai launuka daban-daban.

Source: Facebook
Abin da dokokin hukumar suka tanada
Masana harkar sufurin jiragen sama sun ce bayanin jami'an tsaron ya haifar da tambayoyi masu yawa kan bin dokokin tsaro na kasa da na duniya.
Dokokin sufurin jiragen sama na Najeriya sun tanadi cewa yankunan da jirage ke aiki wurare ne masu matukar kariya, inda sai masu izini ko fasinjoji masu takardun tafiya kadai ake bari, cewar Leadership.
Masana sun tambayi dalilin da ya sa jami'an tsaro suka dogara da bayanin baki kawai ba tare da tabbatar da katin shiga jirgi ko wasu takardun tafiya ba.
Majiyoyi daga cikin ma'aikatar sun ce irin wannan matsala na da alaka da al'adar fifita manyan mutane, inda wasu jami'ai ke sassauta matakan tsaro ga masu fada a ji.
Ana sa ran binciken zai duba rawar da jami'an tsaron jiragen sama suka taka wajen ba da damar shiga wuraren da aka haramta a lokuta daban-daban.
Minista Keyamo ya rubuta wasika ga Trump
Mun ba ku labarin cewa Ministan Harkokin Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo ya aika budaddiyar wasika ga Shugaba Donald Trump kan zargin kisan kiristoci.
Keyamo SAN ya bayyana cewa wannan zargi ba gaskiya ba ne domin matsalar tsaron Najeriya ta shafi kiristoci da musulmai
Hakan ya biyo bayan ci gaba da maida martani ga Shugaban Amurka, Donald Trump bayan ya yi barazanar kawo farmaki don kare kiristocin Najeriya.
Asali: Legit.ng

