Mai Neman Takara a NNPP Ya Zargi Kwankwaso da 'Cinye' Masa Kudi Lokacin Zaben 2023
- Atiku Abubakar Isah ya yi sha’awar zama wakilin mutanen mazabar Ida / Ibaji / Ofu / Egalamela a majalisar tarayya
- ‘Dan siyasar ya ce shi kadai aka saidawa fam, amma aka tsaida wanda yake ya fi kashewa jam’iyyar NNPP kudi a 2023
- Atiku Abubakar ya ce dama saboda Rabiu Kwankwaso ya shigo NNPP, kuma ya ce ba zai je neman hakkinsa a kotu ba
- Matashin tsohon 'dan Kwankwasiyya ne, kafin abubuwa su canza daga baya, Legit Hausa ta yi hira ta musamman da shi
Legit.ng Hausa ta bude tasha a manhajar Whatsapp. Kasance tare da mu don samun rahotanni da dumi-dumi!
M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.
Abuja - Atiku Abubakar wani ‘dan siyasa ne mai tasowa a jihar Kogi, ya taso jagoran NNPP, Rabiu Musa Kwankawso a gaba.
‘Dan siyasar ya nemi tikitin tsayawa takarar ‘dan majalisa mai wakiltar Ida/Ibaji/Ofu/ Egalamela a NNPP, sai dai bai dace ba.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/c964db05c20273e3.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
‘Dan siyasa ya goyi bayan Ganduje, ya ce shi ya fi dacewa da shugabancin jam’iyyar APC
![Kwankwaso Kwankwaso](https://cdn.legit.ng/images/1120/71d7e24db9b8df8c.jpeg?v=1)
Asali: Facebook
Atiku ya saye fam a NNPP a 2023
Atiku Abubakar ya yi ikirarin ya saye fam a jam’iyyar NNPP domin zaben 2023, amma a karshe aka maye gurbinsa da wani.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng
Atiku ya ce shi kadai jam’iyyar NNPP ta saidawa fam ya nemi kujerar ‘dan majalisar Ida/ Ibaji/Ofu/Egalamela a zaben da ya wuce.
A cewarsa, daga baya sai ya ji wani wanda bai yanki takardar shiga neman takara ba ne ya samu tuta, bayan ya gama kashe kudi.
Atiku zai kai Kwankwaso/NNPP kotu?
‘Dan siyasar ya shaidawa Legit cewa duk abin da ake yi, ya ki ya shigar da kara a kotu kuma a karshe APC ta lashe zaben a Kogi.
Da mu ka nemi jin ko nawa ya kashe, ya ce ya batar da kusan N1.2m, amma babu abin da ya yi masa ciwo kamar bata masa lokaci.
![](https://cdn.legit.ng/images/360x203/ae5348f630701060.jpeg?v=1)
Kara karanta wannan
Emefiele: “Yadda na biya cin hancin $600, 000 domin a biya ni kudin kwangila a CBN”
“Mun zauna da shi (Rabiu Musa Kwankwaso), ya nuna mani ni ne ‘dan takaran majalisa.”
“Abin da ya fi bata mani rai shi ne yadda aka bar ni a je ina ta surutu cewa na samu tikiti.”
Kwankwaso da kudin fam a NNPP
Sai dai a ka’ida ba Kwankwaso yake da hakkin kula da kudin sayen fam a NNPP ba, ‘dan siyasar ya ce ya zauna da shugabannin jam’iyyar.
Atiku ya ce ya yi zama da shugabannin NNPP na kasa a lokacin, amma hakan bai sa an rage masa asarar da ya yi wajen shiga zaben ba.
Duk abin da ya faru, yana ganin sai yadda Kwankwaso ya ce ake yi a NNPP kuma tun farko saboda shi ya shigo jam’iyya mai kayan dadi.
Rikicin da za a iya yi a 2027
A rahoton nan, kun ji cewa shekara da shekaru kenan ana bakar adawa tsakanin ‘Yan darikar Kwankwasiyya da mutanen Gandujiyya.
A Kaduna, ana shuka irin rigima tsakanin Nasir El-Rufai da tsohon yaronsa a siyasa, gwamna Uba Sani bayan an fara kuka game da bashi.
Asali: Legit.ng