El-Rufai @ 64: Abin da Shugaba Tinubu Ya Fada a Kan Tsohon Gwamnan Kaduna

El-Rufai @ 64: Abin da Shugaba Tinubu Ya Fada a Kan Tsohon Gwamnan Kaduna

  • Nasir El-Rufai ya cika shekaru 64 a duniya, masoya da abokan siyasa suna ta aiko masa da sakon murna a wannan lokaci
  • Jawabi na musamman ya fito daga fadar shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu ya taya tsohon gwamnan Kaduna farin ciki
  • Mai taimakawa shugaban Najeriya a kafofin sada zumunta, Olusegun Dada ya fitar da cikakken jawabin Bola Tinubu a X

M. Malumfashi ya shafe shekaru ya na kawo labaran Hausa musamman na siyasa, addini, tarihi, wasanni da al’ada.

Kaduna - A rana irin ta 16 ga watan Fubrairun kowace shekara, ake taya Nasir El-Rufai murnar zagayowar ranar haihuwarsa.

Bola Ahmed Tinubu ya taya Malam Nasir El-Rufai murnar zagayowar wannan rana yayin da ya cika shekara 64 yanzu a duniya.

El-Rufai
Bola Ahmed Tinubu da Nasir El-Rufai a Kaduna Hoto: @officialABAT
Asali: Twitter

Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya fitar da jawabi ta hannun Ajuri Ngalale yana yi wa tsohon gwamnan Kaduna fatan alheri.

Kara karanta wannan

Tinubu ya tura sako mai muhimmanci ga mai dakin Buhari, ya fadi halayenta

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Tinubu ya taya Nasir El-Rufai murna

Mista Olusegun Dada ya wallafa jawabin shugaban kasa a dandalin X a ranar Asabar.

Mai girma shugaban Najeriyan ya yaba da rawar gani da gudumuwar da Nasir El-Rufai ya bada a duka mukaman da ya rike.

Tun daga lokacin da ya rike shugabancin hukumar BPE zuwa zamansa Ministan birnin Abuja, Tinubu ya ce El-Rufai ya yi fice.

Bayan nan ya ce Malam El-Rufai ya yi mulki na shekaru takwas a jere tun daga 2015 zuwa 2023 matsayin gwamna a Kaduna.

A tarihin Kaduna, Ahmad Muhammad Makarfi ne kurum ya dade haka a matsayin gwamna, shekaru kusan 16 da suka wuce.

Abin da Shugaba Tinubu ya fada a kan El-Rufai

"Bola Tinubu yana aika sakon murna ga tsohon gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir Ahmad El-Rufai a lokacin murnar zagayowar ranar haihuwarsa a ranar 16 ga Fubrairu, 2024."

Kara karanta wannan

Ribadu: Bayanai sun fito bayan kus-kus da Hadimin Tinubu yayi da Sanatoci a Majalisa

"Tinubu ya jinjinawa irin shugabanci da fitattun gudumuwar da kwararren shugaban ya nuna a kasar a tsawon rayuwarsa a aikin gwamnati a matsayin gwamna sau biyu a karkashin APC, tsohon Darekta Janar a BPE kuma tsohon Ministan harkokin Abuja."

- Ajuri Ngalale

A jawabinsa, shugaban Najeriyan ya nuna yana fata tsohon gwamnan zai cigaba da zama abin koyi ga ‘yan baya masu tasowa a yau.

Shugaba Tinubu ya yi wa tsohon sakataren na jam’iyyar APC mai mulki fatan koshin lafiya.

An hana El-Rufai Minista

A wani lamari mai kama da tuggun siyasa, ana da labarin yadda aka hana Malam Nasir El-Rufai sake zama Minista a gwamnatin nan.

Tun farko El-Rufai bai taba nuna kwadayin Bola Tinubu ya ba shi mukami ba, sai dai ma ya nuna ya fi sha'awar ya tsaya daga gefe guda.

Asali: Legit.ng

Online view pixel