An Barke da Murnar Nasarar Gwamna Abba a Jihar Nasarawa, An Tura Muhimmin Sako Ga Kotun Koli

An Barke da Murnar Nasarar Gwamna Abba a Jihar Nasarawa, An Tura Muhimmin Sako Ga Kotun Koli

  • Ana cigaba da murnar nasarar da gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya samu a Kotun Ƙoli kan Nasiru Gawuna
  • Magoya baya da mambobin ƙungiyar Kwankwasiyya sun bi sahu wajen gudanar da nasu bikin a jihar Nasarawa
  • Sun nuna farin cikinsu kan nasarar da gwamnan ya samu tare da yin kira da Kptum Ƙoli ta yi adalci a shari'ar zaɓen gwamnan Nasarawa

Editan Legit Hausa Sharif Lawal yana da ƙwarewar shekaru wajen kawo rahotannin siyasa, al'amuran yau da kullum, tsegumi da nishaɗi

Jihar Nasarawa - Mambobi da magoya bayan ƙungiyar Kwankwasiyya a ranar Laraba sun yi dandazo a ƙaramar hukumar Keana ta jihar Nasarawa.

Magoya bayan na ƙungiyar Kwankwasiyya sun taru ne domin murnar nasarar da gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya samu a Kotun Ƙoli, cewar rahoton jaridar The Punch.

Kara karanta wannan

Shugaba Tinubu ya fadi hanya 1 da zai bi wajen magance matsalar rashin tsaro a Najeriya

An yi bikin murnar nasarar Gwamna Abba a Nasarawa
Magoya bayan Kwankwasiyya sun yi murnar nasarar Gwamna Abba a jihar Nasarawa Hoto: Rabiu Musa Kwankwaso
Asali: Facebook

Da yake jawabi a ranar Laraba yayin bikin murnar nasarar da gwamnan ya samu, shugaban ƙungiyar a ƙaramar hukumar Keana ta jihar, Usman Dikko, ya yabawa shugaban ƙasa Bola Tinubu kan rashin tsoma bakinsa a hukuncin kotun.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Ya ƙara da cewa matakin da ya ɗauka zai taimaka wajen ƙarfafa dimokuradiyya a ƙasar nan, rahoton von.gov.ng ya tabbatar.

Wacce buƙata suka nema a wajen Kotun Ƙoli?

Ya kuma buƙaci Kotun Ƙoli ta yanke hukunci na gaskiya a rikicin zaɓen gwamnan jihar Nasarawa domin tabbatar da zaman lafiya da haɗin kan jihar.

A kalamansa:

"Gwamnan jihar Kano cikakken ɗan Kwankwasiyya ne, shi ya sa muka taru domin murnar nasarar da ya samu a Kotun Ƙoli. Ko da yake an fuskanci ƙalubale a kotun sauraron ƙararrakin zaɓe da kotun ɗaukaka ƙara, mun yi farin ciki da nasarar da ya samu daga ƙarshe.

Kara karanta wannan

Uba Sani da sauran cikakken jerin gwamnonin da Kotun Koli za ta yanke hukunci kan nasararsu

"Muna so mu gode wa Shugaba Tinubu kan rashin tsoma baki a shari'ar da kuma barin wanda ya yi nasara a zaɓen ya zama shi ne ya yi nasara a kotun.
"Muna roƙon cewa kamar yadda alƙalan Kotun Ƙoli suka duba shari’ar jihar Kano da idon basira, su duba lamarin Jihar Nasarawa a tsanake, su tabbatar da nasarar wanda mutane suka zaɓa domin samar da zaman lafiya a jihar."

Jigon NNPP Ya Faɗi Dalilin Tinubu Na Ƙin Tsoma Baki a Shari'ar Kano

A wani labarin kuma, kun ji cewa wani jigo a jam'iyyar NNPP ya bayyana dalilin da ya sanya Tinubu ya ƙi tsoma baki a shari'ar zaɓen gwamnan Kano.

Honorabul Danlami Kubau ya bayyana cewa shugaban ƙasan ya ƙi tsoma baki me saboda dimokuraɗiyyar ƙasar nan.

Asali: Legit.ng

Online view pixel