Kotun Koli Ta Yi Hukunci Kan Shari'ar Neman Kifar da Gwamna APC, Ta Bayyana Dalilai

Kotun Koli Ta Yi Hukunci Kan Shari'ar Neman Kifar da Gwamna APC, Ta Bayyana Dalilai

  • Yayin da aka yanke hukuncin zaben gwamnoni da dama a Abuja, Kotun Koli ta raba gardama a zaben jihar Cross River
  • Kotun ta tabbatar da Gwamna Bassey Otu na jami'yyar APC a matsayin halastaccen gwamnan jihar
  • Har ila yau, kotun ta yi fatali da korafe-korafen dan takarar jam'iyyar PDP, Sandy Onor saboda rashin gamsassun hujjoji

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

FCT, Abuja - Kotun Koli da ke birnin Tarayya Abuja ta yi hukunci kan zaben gwamna jihar Cross River.

Kotun ta yi fatali da korafe-korafen dan takarar jam'iyyar PDP, Sandy Onor saboda rashin gamsassun hujjoji.

Kotun Koli ta raba gardama kan shari'ar zaben jihar Cross River
Kotun Koli ta tabbatar da nasarar Gwamna Bassey Otu. Hoto: Bassey Otu.
Asali: Twitter

Wane hukunci kotun ta yanke kan shari'ar?

Kara karanta wannan

Kotun Koli ta yi hukunci kan shari'ar neman tsige gwamnan APC, bayanai sun fito

Har ila yau, ta ayyana Gwamna Bassey Otu a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna a jihar, TheCable ta tattaro.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Hukumar INEC ta tabbatar da Bassey Otu na jam'iyyar APC a matsayin wanda ya yi nasara a zaben da aka gudanar a watan Maris.

Yayin hukuncin, Mai Shari'a, Helen Ogunwumiju ya ce wannan korafi ba ya da tushe kuma ba ta wa bangaren shari'a lokaci ne.

Wane hukunci aka yanke a watan Satumba a jihar?

Sai dai a watan Satumbar 2023, Otu ya sha kaye a hukuncin kotun sauraran kararrakin zabe jihohi da aka gudanar.

Otu ya samu nasarar zaben gwamnan jihar da kuri'u 258,619 a kananan hukumomi 15 daga cikin 18 da ke jihar.

Yayin da dan takarar jam'iyyar PDP, Onor da ke biye da shi a matsayin na biyu ya samu kuri'u 179,636 a zaben, kamar yadda Channels TV ta tattaro.

Kara karanta wannan

Bayan na Kano, Kotun Koli ta raba gardama kan shari'ar gwamnan PDP a Arewa, ta fadi dalili

Kotu ta yi hukunci a zaben Cross River

A wani labarin, Kotun Daukaka Kara ta raba gardama kan tababar da ake yi a shari'ar zaben gwamnan jihar Cross River.

Kotun ta tabbatar da nasarar Gwamna Bassey Otu na jam'iyyar APC a matsayin zababben gwamnan jihar da aka gudanar a watan Maris.

Har ila yau, Kotun ta yi fatali da korafe-korafen dan takarar jam'iyyar PDP, Sandy Onor saboda rashin hujjoji.

Asali: Legit.ng

Online view pixel