Cikakken Sunayen Jiga-jigan APC da Ke Dakon Kujerar Minista Lalong Idan Ya Koma Sanata

Cikakken Sunayen Jiga-jigan APC da Ke Dakon Kujerar Minista Lalong Idan Ya Koma Sanata

Jiga-jigan jami'yyar APC a jihar Plateau sun fara nuna kwadayinsu kan neman kujerar Sanata Simon Lalong.

Abdullahi Abubakar, Editan Legit Hausa ne a bangaren siyasa, kasuwanci da al'amuran yau da kullum ne, ya na da gogewar aikin jarida sama da shekaru uku.

A kwanakin nan Lalong ya ce bai yanke shawara ba kan ci gaba da zama a matsayin Minista ko kuma Sanata a Najeriya.

Jerin jiga-jigan jam'iyyar APC da ke hankoron kujerar Minista Lalong
Minista Lalong na tunanin barin kujerar Minista zuwa Sanata. Hoto: C. Dakas, Simon Lalong, Ezikiel Nyam.
Asali: Facebook

Jiga-jigan APC da ke neman kujerar Lalong

Lalong dai ya yi nasara a Kotun Koli bayan ya samu mukamin Minista a gwamnatin Bola Tinubu.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

Legit ta jero muku wasu daga cikin masu son gadar kujerar tashi.

1. Farfesa Sale Kanam

Ana hasashen Kanam wanda tsohon shugaban karamar hukumar Kanam ne zai iya samun wannan dama ta kujerar Minista.

Kara karanta wannan

‘Yan APC sun fara harin matsayi tun da Ministan Tinubu ya hango kujerar Sanata

Farfesan na samun goyon baya daga Yusuf Gagdi da ke wakiltar mazabar Kanam/Pankshin/Kanke a jihar.

2. Farfesa Dakas Dakas

Dakas wanda tsohon kwamishinan Shari'a ne a mulkin tsohon Gwamna Lalong zai iya samun damar maye gurbin mai gidansa.

Masana sun ce kwarewar Dakas a bangaren Shari'a da kuma gudunmawar da ya bayar wurin sauya kundin tsarin jami'yyar ka iya ba shi dama.

3. Farfesa Danladi Atu

Tsohon Sakataren Gwamnatin Lalong ya na samun goyon baya daga mai gidansa.

Sai dai masana sun ce rashin samun goyon bayan jama'a idan aka kwatanta da sauran na iya kawo masa cikas a mukamin.

4. Farfesa Garba Sharabutu

Sharabutu wanda shi ne sakataren hukumar ARCN ana hasashen zai iya maye gurbin tsohon gwamnan jihar, Simon Lalong.

5. Komsol Alpanson

Alpanson wanda tsohon dan Majalisar Tarayya ne ka iya gadar kujerar ganin yadda ya ke da mutane a jihar.

Sai dai wasu sun yi korafin cewa zai iya rasa damar saboda rashin goyon bayan dan takarar APC a jihar.

Kara karanta wannan

Sanatoci sun burge, sun ba da albashinsu gaba daya ga 'yan maulidin da harin soji ya shafa

6. Festus Fuanter

Festus shi ne mataimakin sakataren APC ta kasa wanda ke da hasken samun mukamin ganin yadda ya ke da alaka mai karfi da shugabannin jam'iyyar ta kasa.

7. Rufus Bature

Bature wanda shi ne shugaban jam'iyyar APC a jihar wanda magoyin bayan Tinubu ne na hakika zai iya samun damar gadar kujerar Lalong, cewar Daily Trust.

8. Bashir Musan Santi

Tsohon Sakataren jam'iyyar APC, Santi da kuma Sani Mudi, tsohon hadimin Lalong da su ka fito daga Jos ta Arewa ka iya samun kujerar Minista.

Lalong ya fara kokwanto kan kujerar Minista

A wani labarin, Ministan Kwadago Simon Lalong na tunanin barin kujerar Minista.

Lalong ya bayyana cewa ya shiga rudani da rashin tabbas kan wace kujera zai zaba.

Asali: Legit.ng

Online view pixel