Gwamnoni 3 da Suka Auka Matsalar Zabe Bayan Yin Fito Na Fito da Buhari a Kan Canjin Kudi

Gwamnoni 3 da Suka Auka Matsalar Zabe Bayan Yin Fito Na Fito da Buhari a Kan Canjin Kudi

  • Akwai wasu fitattun Gwamnoni da suka kalubalanci gwamnatin tarayya a kan batun canza manyan kudi
  • Bello Matawalle ya fito fili ya na cewa matsayar da ya dauka ce ta jawo sanadiyyar rashin nasararsa
  • Gwamnonin jihohin Kaduna da Kano sun garazaya kotun koli, a karshe ba su ji dadin sakamakon zabe ba

A rahoton nan, Legit.ng Hausa ta dauko Gwamnonin da suka fi zakewa wajen yin fada da gwamnati kan canjin kudin da yadda ta kaya da su a zabe.

Gwamnonin da suka yi asara

1. Abdullahi Umar Ganduje

Guguwar Rabiu Musa Kwankwaso a NNPP tayi wa Gwamna Abdullahi Umar Ganduje illa a zaben bana, jam’iyyarsa ta rasa mulki bayan nasarar Abba Kabir Yusuf.

Baya ga zaben Gwamna, NNPP ta karbe kujerun Sanatoci biyu na Kano da ‘yan majalisar wakilan tarayya da-dama, haka lamarin yake a zaben majalisar dokoki.

Kara karanta wannan

Zaben Kogi: Jerin jiga-jigan siyasan APC 3 da ke son maye gurbin Yahaya Bello da tasirinsu

Kafin zaben, Abdullahi Umar Ganduje ya caccaki Muhammadu Buhari, ya zarge shi da yunkurin kawo matsala ga jam’iyyar da ta taimakasa ya iya lashe zabe.

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

2. Nasir El-Rufai

Malam Nasir El-Rufai yana cikin ‘yan gaba-gaba wajen yin shari’a da gwamnatin tarayya a dalilin hana amfani da tsofaffin kudi da bankin CBN ya nemi ya yi.

A zaben 2023, PDP tayi nasara a zaben Shugaban kasa a Kaduna, sannan jam’iyyar adawar ta karbe duka Sanatoci uku da ke jihar da ‘yan majalisan wakilai goma.

Gwamnoni
Shugaban kasa tare da Gwamnoni a Aso Rock Hoto: www.herald.ng
Asali: UGC

Malam Uba Sani ya sha da kyar ne a zaben Gwamna da aka yi. PDP da Nasir El-Rufai ya yi wa kaca-kaca a 2019 ta samu kujerun majalisar dokoki da-dama a bana.

3. Bello Matawalle

Gwamna Bello Matawalle ya na ganin karfin sojoji aka yi amfani da su domin a hana shi zarcewa a kan kujerar Gwamnan Zamfara saboda ya yaki gwamnatin tarayya.

Kara karanta wannan

Akwai Aiki a Gaban NNPP a Kano, APC Za Ta Karbe Nasarar Abba a Zaben Gwamnan 2023

Dr. Dauda Lawal Dare ya doke Bello Matawalle a kananan hukumomin Anka, Bukkuyum, Bungudu, Gummi, Gusau, Kaura, Maru, Shinkafi, Tsafe da Zurmi

Jam’iyyar APC ta iya samun nasara ne kurum a Bakura, Birnin Magaji, Mafara da Muradun, yankunan da Gwamna, Abdulaziz Yari da Ahmad Sani Yarima suka fito.

Jihar Kogi

Gwamna Yahaya Bello ya tsaya tsayin-daka wajen kalubalantar hana amfani da tsofaffin kudi da aka yi, hakan bai hana jam’iyyar APC galaba a jihar Kogi ba.

Sai daga baya za ayi zaben sabon Gwamna a Kogi, zuwa lokacin Muhammadu Buhari ya bar ofis.

Rikici a APC ta Delta

Rahoton da aka fitar a baya, ya nuna cewa wasu shugabannin APC na reshen jihar Delta sun kori Sanata Ovie Omo-Agege a matsayin ‘dan jam’iyya mai-ci.

An zargi Ovie Omo-Agege da aikata laifuffuka da-dama da yi wa jam’iyya zagon-kasa, tare da yin aika-aikar da ta jawowa jam’iyya abin kunya a zaben bana.

Kara karanta wannan

Zaben gwamnan 2023: Taya Murnar Nasir Yusuf Gawuna Ga Abba Kabir Yusuf Gida-Gida

Asali: Legit.ng

Online view pixel