'Yar Gwamna Mai-Ci da Jerin Duka Mata 45 da Za Su Tafi Majalisar Dokoki a Jihohi 21

'Yar Gwamna Mai-Ci da Jerin Duka Mata 45 da Za Su Tafi Majalisar Dokoki a Jihohi 21

  • Mutane 988 za su tafi majalisar dokoki na jihohi a watan Yunin 2023, amma 48 kacal ne mata a ciki
  • Hakan ya nuna mata ba su kai kashi 5% ba, duk fiye da 47% na masu kada kuri’a a kasar matan ne
  • Ekiti, Kwara, Akwa Ibom su na cikin jihohin da mata suka samu kaso mai yawa a majalisar dokoki

Abuja - Wani dogon rahoto na Daily Trust ya tattaro matan da suka yi nasara a zaben majalisar dokoki da aka shirya a bana, su na jiran gado.

A jihohi 21 ne mata suka samu akalla kujera daya a majalisar dokoki, daga cikin su akwai Anambra, Kaduna, Bayelsa, Benuwai da Kuros Riba.

Sauran jihohin su ne Delta, Ekiti, Oyo, Taraba, Nasarawa, Filato, Kogi, Kwara, Akwa Ibom. Akwai Ogun, Legas, Adamawa, Ondo, Enugu da Ebonyi.

Kara karanta wannan

Muhimman Abubuwa 7 Game Da Tsohon Hafsan Hafsoshin Soji Na Zamanin Abacha, Laftanar Janar Diya

Jihohin da mata zalla ne za su kawo dokoki daga 2023 zuwa 2027 su ne: Bauchi, Borno, Gombe, Imo, Jigawa, Kano, Katsina, Kebbi, Niger, da Abia.

Kamar yadda jaridar ta kawo rahoto a ranar Lahadi, ragowar sun hada da: Osun, Rivers, Sokoto, Yobe da Zamfara, fiye da 70% duka a Arewa ne.

Anambra

DUBA: Bibiyemu a Instagram don samun labarai masu muhimmanci kai tsaye cikin manhajar

1. Mrs Nkechi Ogbuefi Anaocha)

Enugu

2. Hon Princess Obiajulu Ugwu (Enugu ta Kudu)

3. Hon Jane Ene (Udi ta Arewa)

Bayelsa

4. Egba Ayibanegiyefa (Yenagoa I)

5. Mrs Ebizi Ndiomu Brown (Sagbama II)

Benuwai

6. Mrs Lami Danladi (Ado)

7. Mrs Becky Orpin (Gboko ta Gabas)

Kuros Ribas

8. Rita Ayim (Ogoja)

Delta

9. Marilyn Okowa (Ika ta Arewa)

10. Bridget Anyafulu (Oshimili ta Kudu)

Ekiti

11. Mrs Bolaji Egbeyemi Olagbaju (Ado I)

12. Okuyiga Eyiyato Adeteju (Ayekire/Gbonyin)

13. Olowokere Bose Yinka (Efon)

14. Ogunlade Maria Abimbola (Emure)

15. Fakunle Okiemen Iyabo (Ilejemeje)

Kara karanta wannan

Yadda Rikicin 'Yan PDP da Gwamna a Arewa Suka Jawo Fasto Ya Ci Zaben Gwamna

16. Abimbola Solanke (Moba I)

Majalisa
Matan da za su je Majalisa Hoto: www.bellanaija.com, thenationonlineng.net, kyp247.com
Asali: UGC

Edo

17. Maria Edeko Omozele (Esan ta Arewa maso Gabas)

Oyo

18. Olajide Olufunke Comforter (Ibadan ta Arewa)

19. Bisi Oluranti Oyewo Micheal (Ogbomosho ta Arewa)

Taraba

20. Hajiya Batulu Muhammed (Gashaka)

21. Borinica Alhassan (Bali)

Nasarawa

22. Hajara Ibrahim (Nasarawa ta Tsakiya)

Filato

23. Happiness Akawu (Pengana)

24. Salomi Tanimu (Pankshin ta Kudu)

Kogi

25. Mrs Comfort Ojoma Nwuchola (Ibaji)

26. Mrs Omotayo Adeleye-Ishaya (Ijumu)

Kwara

27. Rukayat Shittu (Owode/Onire)

28. Arinola Lawal (Ilorin ta Gabas)

29. Medinat AbdulRaheem (Lanwa/Ejidongari)

30. Aishat Babatunde-Alanamu (Ilorin ta Arewa maso yamma)

31. Mariam Aladi (Ilorin ta Kudu)

Akwa Ibom

32. Selong Precious Akamba (Urua Offong Oruko)

33. Etim Itorobong Francis (Uruan)

34. Onofiok Kenim Victor (Oron/Udung Uko)

35. Ukpatu Selinah Isotuk (Ikot Abasi/Obolo ta Gabas)

Ogun

36. Bolanle Lateefat Ajayi (Egbado ta Kudu)

37. Bakare Omolola Olanrewaju (Ijebu Ode)

Adamawa

38. Kate Raymond Manuno (Demsa)

Ondo

39. Witherspoon Atinuke Morenike (Owo I)

40. Fayemi Olawunmi Annah (Ilaje)

41. Ogunlowo Oluwaseun (Idanre)

Ebonyi

42. Mrs Esther Agwu (Ohaukwu ta Arewa)

Kara karanta wannan

Saura Watanni 2 Ya Bar Ofis, Buhari Ya Karfafi Muhimmin Aikin da Ya Tattago a Arewa

43. Chinyere Nwagbaga (Ebonyi ta Arewa)

Kaduna

44. Mrs Comfort Amwe (Sanga)

45. Munira Suleiman Tanimu (Lere ta Gabas)

Mata 6 sun zama 'Yan majalisa

Rahoto ya zo a baya cewa Uwargidar Gwamnan Ekiti, Olayemi Oyebanji ta ji dadin ganin sakamakon zaben ‘Yan majalisar dokoki na bana.

Uwargidar jihar ta Ekiti tayi farin cikin samun labari cewa Bose Olowookere, Bolaji Olagbaju, Abimbola Solanke da wasu mata za su je majalisa.

Asali: Legit.ng

Online view pixel