Saura Watanni 2 Ya Bar Ofis, Buhari Ya Karfafi Muhimmin Aikin da Ya Tattago a Arewa

Saura Watanni 2 Ya Bar Ofis, Buhari Ya Karfafi Muhimmin Aikin da Ya Tattago a Arewa

  • Gwamnatin tarayya ta amince a batar da N453.90bn wajen sayen kayan aikin titin jirgin kasa
  • Kamfanin Kamfanin MSSRs Mota-Engil Nigeria Ltd yana gina hanyar jirgin kasan Kano-Maradi
  • A taron da shugaban kasa ya jagoranta, an amince da takardun da Ma’aikatar sufuri ta kawo

Abuja - Gwamnatin tarayya ta yi na’am da kashe N453.90bn domin sayen kayan aiki da na gyare-gyaren dogon Kano zuwa Maradi da ake ginawa.

Majalisar zartarwa watau FEC ta amince da wannan mataki a zaman da aka yi na ranar Larabar nan, labarin ya fito ne a jaridar Punch ta kasar nan.

Kudin da aka amince a batar a taron FEC din sun hada da N510.93m na sayen motocin kwana-kwana na kashe wuta a tashoshin Fatakwal da Legas.

Mai girma Ministan sufuri na kasa, Mu’azu Sambo ya tabbatar a wannan a lokacin da yake zantawa da manema labarai a karshen zaman da aka yi a jiya.

Kara karanta wannan

Sanatan Jihar Kano Ya Shiga Sahun Masu Neman Kujerar Majalisar Dattawa a 2023

Aikin jirgin Kano - Maradi

A shekarar 2021 aka dauko wannan aikin jirgin kasa na kilomita 284 wanda zai ratsa Kano zuwa Kazaure, Bauchi, Daura, Mashi, Katsina har Jibiya.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Aikin zai karkare ne a garin Maradi da ke Jamhuriyyar Nijar, kasar da ke iyaka da Katsina.

Taron FEC
Taron FEC a Aso Rock Hoto: @Buhari Sallau
Asali: Facebook

A wancan lokacin, Rotimi Amaechi an ce titin zai kunshi tashohi 15, kuma ana ran a rika samun fasinjoji 9364 a rana dauke da metric ton 3000 na kaya.

Jawabin Ministan sufuri

An rahoto Mu’azu Sambo yana cewa sun bijiro da batun wannan kwangila a gaban Ministocin tarayya domin amincewa a sayo wasu kayayyakin aiki.

Ma’aikatar sufurin ta nemi amincewar FEC domin a saye kayan gyaran dogon, kuma an amince. Kamfanin MSSRs Mota-Engil Nigeria Ltd suke aikin.

Ministan ya ce sun gabatar da takarda a madadin NPA domin kamfanin All Works Commercial Company Limited ya samar da motocin kashe gobara.

Kara karanta wannan

Binani: Minista Ya Yi Maganar Makarkashiyar da PDP ke Shiryawa a Zaben Adamawa

Ministan gona na kasa, Mohammed Abubakar, ya yi wa manema labarai magana yana cewa FEC ta yi na’am da takardun da suka gabatar a zaman.

Shari'ar Atiku Abubakar v PDP

A rahoton da mu ka fitar a baya, an ji Lauyoyin Atiku Abubakar sun sha alwashin sai sun karbe nasarar da Bola Tinubu ya samu a zaben 2023

Babban Lauyan ‘Dan takaran, Joe-Kyari Gadzama ya ce INEC sun rika tace sakamako kafin a daura IRev, wanda hakan ya jawo APC tayi magudi.

Asali: Legit.ng

Online view pixel