Ministan Buhari Ya Fayyace Komai Bayan An Ga Babu Sunansa Cikin Lauyoyin Tinubu

Ministan Buhari Ya Fayyace Komai Bayan An Ga Babu Sunansa Cikin Lauyoyin Tinubu

  • Da farko an yi tunanin Festus Keyamo SAN yana cikin Lauyoyin da za su ba Bola Tinubu kariya
  • Lauyan ya ce tun da shi Minista ne, ba zai iya tsayawa ‘dan takaran ba sai ya sauka daga kujera
  • Amma mutane sun shiga yi wa Keyamo raddi cewa yana kujerar Ministan, ya shiga siyasa

Abuja - Festus Keyamo wanda babban Lauya ne da ya kai matsayin SAN, ya dauki lokaci ya yi karin-haske a kan batun shari’ar zaben shugaban kasa.

Ganin cewa ba a ga Festus Keyamo SAN a jeringiyar Lauyoyin da za su tsayawa Asiwaju Bola Tinubu a kotun zabe ba, wannan ya jawo abin magana.

Lauyan ya yi amfani da shafinsa na Twitter a ranar Talata, ya fadi abin da ya ba zai iya kare ‘dan takaran APC kuma zababben shugaban kasar a kotu ba.

Kara karanta wannan

Ministan Buhari Ya Fadi Babban Dalilin Da Yasa Baya Cikin Manyan Lauyoyin Da Za Su Kare Tinubu

Keyamo ya nuna a matsayinsa na wanda yake rike da mukami a gwamnatin tarayya, bai da damar da zai shiga kotu domin ya ba daidaikun mutane kariya.

Babu ruwan Minista da karar zabe

Tun a 2019 ne Shugaba Muhammadu Buhari ya nada Lauyan a matsayin Minista a ma’aikatar Neja-Delta, daga baya ya koma ma’aikatar kwadago.

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A daidai lokacin da yake Ministan gwamnati, Daily Trust ta rahoto masanin shari’ar yana cewa ba zai iya shiga kotu ba har sai ya sauka daga kujerarsa.

'Yan APC
'Yan APC wajen kamfe Hoto: @officialasiwajubat
Asali: Facebook

Iyakar gudumuwar da Keyamo ko wani Minista da ya kai matakin SAN a Lauya zai iya ba Bola Tinubu a yanzu shi ne a wajen shirye-shiryen shiga kotu.

Maganar Festus Keyamo a Twitter

"Ga masu aiko da tambaya, a kundin tsarin mulkin kasarmu, Ministan tarayya mai-ci ba zai iya shiga cikin tawagar Lauyoyi masu zaman kan su ba.

Kara karanta wannan

Sabon Harin Zamfara Da Kano: Tinubu Ya Yi Allah Wadai, Ya Ce Dole a Takawa Kashe-Kashe Birki a Najeriya

Sai dai Ministan ya/ta taimaka wajen shiryawa shari’a. Saboda haka Ministocin da sun kai matsayin SAN ba za su iya shiga shari’ar zabe ba sai bayan 29 ga watan Mayu."

- Festus Keyamo

Irinsu Harry Iwuala ba su kyale kakakin kwamitin yakin neman zaben na APC haka ba, suka ce ai yana kan kujerar ya rike mukaman siyasa a kamfe.

"Minista mai-ci ya je kotu yana so a gurfanar da ‘dan takaran shugaban kasa. Minista mai-ci ya karbi mukami a kwamitin kamfe.
Shi ya rika yin kalaman siyasa da ba su dace da jami’in gwamnati ba. Ko kun san wanene wannan Minista?

- HARRY Iwuala

Rikicin PDP a Katsina

Yayin da ranar zaben Gwamnonin jihohi ya gabato, an ji labari ‘Yan PDP sun yi karar Sanata Yakubu Lado Danmarke da wasu daga cikin ‘yan bangarensa.

Shugabannin jam’iyyar PDP a Katsina su na tuhumar Aminu Yar’dua, da Mustapha Inuwa da zargi kan yadda aka batar da Naira Biliyan 1.05 na yin kamfe.

Kara karanta wannan

Muje zuwa: Sanata ya fadi wulakacin da gwamnan CBN zai gani bayan saukar Buhari

Asali: Legit.ng

Online view pixel