Obi Na Neman Kuri’un Yan Arewa, Ya Sha Alwashin Kawar Da Talauci

Obi Na Neman Kuri’un Yan Arewa, Ya Sha Alwashin Kawar Da Talauci

  • Peter Obi, dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar LP ya daukarwa al'ummar arewa gagarumin alkawari muddin ya ci zabe a 2023
  • Tsohon gwamnan na jihar Anambra ya ce zai fitar da yankin arewacin kasar daga kangin talauci wanda yayi masu katutu
  • Obi zai aiwatar da hakan ne ta hanyar mayar da hankali ga bangaren noma tare da daga darajar amfanin gonar kafin a fitar da su kasashen waje

Abuja - Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour Party (LP), Mista Peter Obi, ya fara zawarcin al'ummar yankin arewa, wanda ake zargin sune cibiyar talauci a kasar.

Obi wanda ke takara tare da Datti Baba-Ahmed ya daukin alkawarin cewa idan har aka zabe shi a 2023, gwamnatinsa za ta fitar da yankin daga kangin talauci, jaridar Vanguard ta rahoto.

Kara karanta wannan

Daga Karshe, Kungiyar Matan Zamfara Sun Ayyana Wanda Zasu Zaba Tsakanin Atiku da Tinubu a 2023

Peter Obi
Obi Na Neman Kuri’un Yan Arewa, Ya Sha Alwashin Kawar Da Talauci Hoto: Daily Trust
Asali: UGC

Kakakin kungiyar yakin neman zaben Obi-Datti, Dr. Yunusa Tanko, wanda ya yi magana a madadin ubangidansa, ya bayyana hakan ne a wani shirin kai tsaye Na gidan radiyon Bright FM Abuja, a ranar Asabar.

Tanko ya ce Obi wanda ya rike mukamin gwamnan jihar Anambra sau biyu, ya kudurci aniyar sauya labarin Najeriya zuwa mai kyau.

Shin kana da labarin da ka/ki ke son an wallafa ma ka/ki? Ka tuntubemu a info@corp.legit.ng!

Obi zai bunkasa harkar noma a arewacin kasar

A cewarsa, dan takarar da tawagarsa masu kishin kasa sun fahimci tarin albarkatun da ke arewacin Najeriya musamman ma a bangaren noma don haka sun dauki aniyar mayar da hankali sosai kan noma don fitar da al’ummar yankin daga kangin talauci.

Tanko ya bayyana cewa ba a bangaren yin noma kadai Obi zai mayar da hankali ba harma da tabbatar da ganin amfanin gonar sun kara daraja kafin a fitar da su waje don samun abun da ake bukata don ci gaban kasar.

Kara karanta wannan

2023: Ku Yi Hattara Da Peter Obi, Kungiyar Matasan Kirista Ta Aike Da Sako Mai Karfi Ga Yan Najeriya

Matakin da LP zata dauka don tabbatar da ba a yi magudin zabe ba

Da yake magana game da shirye-shiryen LP don tabbatar da zabe mai inganci, ya yi bayanin cewa jam’iyyar ta fara daukar yan sa-kai.

A cewar Tanko, wadanan yan sa-kan za su yi aiki ba dare ba rana don tabbatar da ganin cewa an tura sakamakon yawan kuri’un da aka kada a kowace rumfa zuwa na’urar hukumar zabe kafin su bar wajen.

Ya ce ana iya zuba yan sa-kan da ya yiwa lakabi sojojin kurkuku a kowace rumfar zabe a fadin kasar kuma za su tsaya har sai an sanar da sakamako sannan an tura su zuwa na’urar INEC.

Obi: Zan fitar da yan Najeriya miliyan 130 daga talauci

Har ila yau, Peter Obi ya yi alkawarin fitar da yan Najeriya miliyan 130 daga talauci idan aka zabe shi a matsayin magajin shugaban kasa Muhammadu Buhari.

Kara karanta wannan

Mataimakin Shugaban Majalissar Dattijai Omo Ovie-Agege Yace Shine Ya Dakatar da Kudirin Tsige Shugaba Buhari

Obi ya bayyana hakan ne bayan ya halarci wani taro a Mkar, karamar hukumar Gboko ta jihar Benue, jaridar Daily Post ta rahoto.

Asali: Legit.ng

Online view pixel