Zaben 2023: Jonathan Zai Goyi Bayan Atiku, Ya Kira Okowa Mataimakin Shugaban Kasa Mai Jiran Gado

Zaben 2023: Jonathan Zai Goyi Bayan Atiku, Ya Kira Okowa Mataimakin Shugaban Kasa Mai Jiran Gado

  • Daga karshe dai, tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya fito fili ya bayyana yan takarar da ya ke goyon baya a 2023
  • Jonathan ya nuna cewa yana tare da jam'iyyar PDP har ma ya kira Gwamna Okowa, mataimakin shugaban kasa mai jiran gado
  • Hakan ya faru ne a yammacin ranar Laraba yayin da Okowa, abokin takarar Atiku, ya jagoranci tawaga ta ziyarci Jonathan a Abuja

FCT, Abuja - Tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan ya goyi bayan takarar shugabancin kasa na Atiku/Okowa a zaben 2023, rahoton The Cable.

Mr Jonathan ya bayyana hakan ne a yayin da tawagar PDP karkashin jagorancin dan takarar mataimakin shugaban kasa Gwamna Ifeanyi Okowa tare da Gwamna Bala Mohammed na Bauchi suka kai masa ziyara a Abuja a yammacin ranar Laraba.

Kara karanta wannan

Rarara Ya Caccaki Ganduje A Sabuwar Waƙa Da Ya Fitar, Lamarin Ya Haifar Da Cece-Kuce A Soshiyal Midiya

Jonathan
2023: Jonathan Ya Kira Okowa Mataimakin Shugaban Kasa Mai Jiran Gado, Ya Ce Yana Tare Da PDP. Hoto: @daily_trust.
Asali: Twitter

LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a info@corp.legit.ng

A wani bidiyo da ya bazu a dandalin sada zumunta, GEJ a matsayinsa na tsohon shugaban kasa ya bayyana Gwamna Okowa a matsayin mataimakin shugaban kasa mai jiran gado.

Mataimakin shugabna kasa mai jiran gado, Jonathan ya kira Okowa

Jonathan ya fada wa Okowa:

"Mataimakin shugaban kasar mu mai jiran gado - ya yi wa'adi biyu a matsayin gwamna."

Mr Jonathan ya kara da cewa a shirye ya ke ya goyi baya tare da yi wa jam'iyyar PDP aiki don ganin ta yi nasara a 2023.

Hakan na nufin cewa tsohon shugaban kasa Jonathan zai goyi bayan Alhaji Atiku Abubakar, dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar ta PDP a 2023.

Jawabin Okowa

A bangarensa, Gwamna Okowa ya ce yana da muhimmanci a nemi goyon baya da albarka daga tsohon Shugaba Jonathan, kuma da albarkarsa jam'iyyar za ta yi nasara a Fabrairu.

Kara karanta wannan

Atiku Abubakar Ya Kinkimo Manya 3 Domin Su Lallabi Wike Ya Marawa PDP baya

Ya ce Jonathan yana da halayen ainihin dattijon kasa, ya kara da cewa sun kai ziyarar ne don tattauna halin da kasa ke ciki da shirin yadda za a ceto kasar a sake gina ta.

Asali: Legit.ng

Online view pixel