2023: Jerin ‘Yan shekara 20 Zuwa 30 da suka Shiga Takarar Majalisar Tarayya

2023: Jerin ‘Yan shekara 20 Zuwa 30 da suka Shiga Takarar Majalisar Tarayya

A wannan rahoto, Legit ta tattaro yadda matasa suka fito neman takarar kujerun siyasa a zaben 2023.

Daga cikin fitattun masu neman takarar majalisar wakilan tarayya akwai Oluwajomiloju Fayose John, Abdussamad Dasuki da Bello El-Rufai.

‘Yan takaran Majalisar Dattawa

A ‘yan shekara 30 masu neman zama Sanatoci a zabe mai zuwa, mafi karancin shekarun da Legit.ng Hausa ta samu shi ne ‘yan shekara 35 a Duniya.

Ga jerin matasan da suka samu tikitin majalisar dattawa a jam’iyyun siyasa, da za su za a gwabza a mazabu dabam-dabam da ake da su a kasar nan a 2023.

1. Ahijo Karlahi Ibrahim

2. Abdulhafiz Saidu

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

Kara karanta wannan

Atiku Ya Sake Shiga Tasku, Wasu 'Ya'Yan PDP Sun Sauya Sheka Zuwa APC Ana Tsaka da Rikici

3. Muhammed Sheriff

4. Ukpong Chuwang Daniel

5. Orok Gloria Odidi

6. Akhimie Kingson

7. Salisu Shamwilu

8. Bala Chichet

9. Yohanna Abimiku

10. Idris Musa Aliyu Nasarawa

11. Fyenda Timlok

12. Muhamma Usman

13. Umar Musa

14. Nubuya Pilinga

15. Musa Ibrahim Idris

16. Isa Buhari

17. Olasupo Ibraheem Olanrewaju

18. Adekunle Elizabeth Oyewumi

19. Urudeen Ojedokun Temileyi

20. Muhammed Gummi

21. Andrew Paul

22. Mumolen Irene Christopher

23. Saidu Ahmed

24. Ulu Joseph

25. Hammadu Ahmadu

'Yan majalisa
Zauren Majalisar Tarayya Hoto: @HouseNgr
Asali: Twitter

Majalisar Wakilan Tarayya

A jihohi irinsu Benuwai, NNPP da ADP sun tsaida matasa suyi takarar majalisar wakilan tarayya.

Legit.ng Hausa ta fahimci a Cross River, Delta, da Ebonyi, akwai masu shekara 30 zuwa 40 da ke takara. A Sokoto, ADC ta tsaida Habiba Gidado mai shekara 29.

Haka zalika a jihar Neja, LP. NRM da APP sun tsaida matasa. Akwai ‘yan kasa da shekara 40 akalla hudu da ke takara a Katsina, haka abin yake a Enugu da Edo.

Kara karanta wannan

Janar Buratai, Tsofaffin Jami’an Tsaro 10 da ke Cikin Kwamitin Yakin Zaben Bola Tinubu

Chiroma Adamu Abidu

Bilyaminu Zaharadeen

Ali Muhammad

Suraja Ahmad Kiyawa

Shuaibu Mudansir Maigatari

Umar Usaini

Rufai Lawal

Alhassan Abdussamadan

Ayuba Jibril

Joseph Justine Zugwai

Zakari Muhammad Ahmad

Muhammad Murtala

Ibrahim Salisu

Abdulhamid Abdulrasheed

Sa’adatu Usman

Siraju Abullahi

Abubakar Yau

Rayyanu Muhammad Kolo

Abubakar Bawuro Rilwan

Habiba Gidado

Tersur Joseph

Muhammad Mustapha Abio

Ali Ahmed Usman

A Kano akwai matasa kusan 30 da ke takarar majalisa a 2023. Mun tattauna da Muktar Mudi Sipikin wanda ya fito takara a mazabar Fagge a karkashin PRP.

A jerin na mu, ba mu kawo sunayen 'yan takaran da suka fito daga jihar Kano ba.

Za mu kai labari - Matasa

Shi ma Yusuf Abdullahi Ahmad wanda aka fi sani da Yusuf Da'awah, ya yi magana a Facebook, yace yana sa ran doke 'dan shekara 62 da mai shekara 59 a Duniya.

Kara karanta wannan

Zaben 2023: Jerin Sunayen Jaruman Fina-Finan Najeriya 24 Da Suka Samu Shiga Kwamitin Kamfen Din Tinubu

Mukhtar Mudi Sipikin yace babu shakka matasa suna fuskantar matsalar kudi, amma suna wayar da kan al’umma su zabi jam’iyyu masu akida a 2023.

Matashin mai shekara 31 yace idan ya zama ‘dan majalisa, zai yi sanadiyyar bude cibiyoyin koyon sana’o’in zamani wanda za su amfana da matasa 8000.

Tarihin NGF a Najeriya

Kun samu labari a shekarar 1999 aka kafa kungiyar, amma babu wanda ya karfafa NGF kamar Dr. Bukola Saraki a lokacin yana Gwamna a jihar Kwara.

Kafin Aminu Tambuwal, gwamnoni irinsu; Rotimi Amaechi, Abdulaziz Yari, da Kayode Fayemi sun rike kujerar shugaban kungiyar NGF a kasar nan.

Asali: Legit.ng

Online view pixel