Tikitin Musulmi da Musulmi: Kungiyar arewa ta jero abubuwa 3 da Tinubu zai fuskanta

Tikitin Musulmi da Musulmi: Kungiyar arewa ta jero abubuwa 3 da Tinubu zai fuskanta

  • Ana ci gaba da takaddama kan zabin Bola Tinubu na daukar Musulmi a matsayin abokin takararsa a zaben 2023 mai zuwa
  • Kakakin kungiyar dattawan arewa ya bayyana cewa babu abun da wannan zabi na Tinubu zai sauya a makomar siyasarsa
  • Tsohon gwamnan na jihar Lagas dai ya tsayar da Sanata Kashim Shettima a matsayin mataimakinsa a babban zaben kasar

Kungiyar dattawan arewa ta yi martani a kan zabar Musulmi da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC), Asiwaju Bola Tinubu, ya yi domin ya zama abokin takararsa a 2023.

NEF ta lissafa wasu abubuwa guda uku da za su faru ga Tinubu a yanzu da ya zabi yin tikitin Musulmi da Musulmi a babban zaben kasar mai zuwa.

Kakakin kungiyar dattawan arewan, Hakeem Baba-Ahmed, ya bayyana cewa wannan mataki da Tinubu ya dauka ba zai kawo kowani sauyi a makomar zabensa ba.

Kara karanta wannan

Muhimman abubuwa 7 da ya dace a sani game da Kashim Shettima, abokin tafiyar Tinubu

Bola Tinubu
Tikitin Musulmi da Musulmi: Kungiyar arewa ta jero abubuwa 3 da Tinubu zai fuskanta Hoto:@officialABAT
Asali: Twitter

A wata wallafa da ya yi a shafinsa na Twitter a ranar Litinin, 11 ga watan Yuli, Baba-Ahmed ya lissafa abubuwa uku da ka iya faruwa.

DUBA: Shigo shafin Legit.ng na manhajar Legit.ng na Telegram! Kada ka bari komai ya wuce ka

  1. Kiristoci za su juyawa tikitin baya.
  2. Daukacin al’ummar Musulmi za su marawa wannan tikiti nasa baya.
  3. Babu wani sauyi da hakan zai kawo ga makomar zabensa.

Naka sai naka: Shugaban kungiyar CAN a Borno ya goyi bayan takarar Shettima

A wani labarin kuma, shugaban kungiyar kiristocin Najeriya reshen jihar Borno, Bishop Mohammed Naga, ya yaba da zabar tsohon gwamnan jihar, Sanata Kashim Shettima da aka yi a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC).

Dan takarar shugaban kasa na APC, Bola Tinubu, ya sanar da Shettima a matsayin abokin takararsa a ranar Lahadi, 10 ga watan Yuli, duk da adawa da aka dunga nunawa kan tikitin Musulmi da Musulmi.

Kara karanta wannan

Tinubu: Abin Da Yasa Na Zabi Musulmi A Matsayin Abokin Takara Na A 2023

Sai dai kuma a wani yanayi da ke nuna goyon bayan takarar Shettima, kungiyar CAN reshen Borno karkashin jagorancin shugabanta ta yi maraba da wannan zabi na Tinubu, jaridar Punch ta rahoto.

Asali: Legit.ng

Online view pixel