Da safiya yau Juma'a, wasu yan bindiga suka kutsa makarantar sakandire a jihar Oyo, inda suka sace shugabar makarantar da dalibai da yawa da ba a tantance ba.
Da safiya yau Juma'a, wasu yan bindiga suka kutsa makarantar sakandire a jihar Oyo, inda suka sace shugabar makarantar da dalibai da yawa da ba a tantance ba.
Rundunar 'yan sanda ta cafke wani mai garkuwa da mutane bayan ya yi yunkurin karbar kudin fansa N10m a jihar Oyo. Masu garkuwar sun sace wani mutum a gidan shi.
'Yan Najeriya za su fara biyan harajin tsaron yanar gizo na kaso 0.5% daga dukkanin kudaden da za su rika turawa ta yanar gizo. CBN ya ba banuna umarnin cire kudin.
Mataimakin shugaban ƙasa, Sanata Kashim Shettima ya soke tafiyar da aka tsara zai wakilci shugaba Tinubu a taron kasuwanci tsakanin Afirka da Amurka a Dellas.
Sanata Abdul'aziz Yar'adua, ƙanin marigayi tsohon shugaban ƙasa, Umaru Musa Yar'adua ya ce ɗan uwansa ya miƙa mulki lokacin da yake jinya amma aka samu matsala.
Hukumar ilimin bai daya (UBEC) ta kaddamar da shirin yiwa malaman karkara 1480 horo na musamman domin bunkasa ilimi. Za a zabi malamai 40 ne daga kowace jiha.
Rundunar ƴan sanda reshen jihar Ondo ta damƙe wani magidanci ɗan shekara 30, Fatai Abdullahi bisa zargin halaka matarsa kan gardamar da suka saba yi koda yaushe.
Da alama dai ziyarar da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya kai kasar Amurka ta haifar da gibi a shugabancin Najeriya. Atiku Abubakar ya yi magana kan hakan.
Dakarun sojojin Najeriya sun samu nasarar fatattakar 'yan ta'adda a jihar Benue bayan sun yi musayar wuta. Jami'an tsaron sun kubutar da mutum biyu.
Gwamnatin tarayya ta yi martani kan wani rahoto da ake yadawa na cewa tana tattaunawa da Amurka da Faransa kan kafa sansanonin sojinsu bayan barin yankin Sahel.
Rundunar 'yan sanda ta tabbatar da harin da 'yan bindiga suka kai a kauyen Ambe da ke karamar hukumar Sanga a jihar Kaduna. Rundunar ta ce an kama dan bindiga 1.
Labarai
Samu kari